A lokacin da shugaba Biden ya fito fili ya bayyana kudurin tsagaita bude wuta a Gaza, da Isra'ila da Amurka suka shirya kuma suka aikewa kungiyar Hamas, ya bayyana hakan ne ba tare da neman amincewar Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ba, in ji wasu jami'an Amurka uku masu masaniya kan lamarin