Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Wakilan Koriya Ta Arewa Sun Kai Ziyara China


Shugaban Koriya Ta Arewa Kim Jong Un
Shugaban Koriya Ta Arewa Kim Jong Un

Kafafen yada labarai sun bada rahoton cewa wani jirgin kasa da ake kyautata zaton ya dauko wakilan, ya bar Beijing yau Talata da rana, kuma an dauki tsauraran matakan tsaro a birnin.

An sami rahoton cewa wata tawagar manyan wakilan Koriya ta Arewa sun kai wata ziyara Beijing, abinda ke ruruta jita-jitan cewa shugaban Koriya Ta Arewa, Kim Jong Un ya gana da jami’an China a babban birnin kasar.

Jaridar Bloomberg, a wani rahoto ta fidda jiya litinin ya ambaci wasu majiyoyi guda 3 da ba a ambata ba, suna cewa shugaba Kim ya kai ziyarar bazata China. Kafafen yada labaran Koriya ta Kudu sun ce kanwar Kim ce ta jagoranci tawagar wakilan, ba shugaban ba.

Babu dai wata sanarwa a hukumance akan rahoton, wanda kafafen China da Koriya Ta Arewa basu ce komai akai ba. In rahoton ya tabbata, to wannan ne zai kasance karon farko da shugaba Kim zai kai ziyara a wata kasa tun bayan da ya fara mulki a shekarar 2011.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG