Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bita: Gudummawar Coci Don Gina Demokradiyya Mai Dorewa A Najeriya


An fadakadda da mabiya addinai da su yi amfani da koyarwan littafi mai tsarki wajen kawo sauyi da zai tsabtace siyasa da kauda cin hanci da rashawa a Najeriya.

A wani taron bita da wata kungiya da ba ta gwamnati ba, House of Issachar ta shirya wa mabiya addinin kirista, mai taken gudummawar Coci wajen gina demokradiyya mai dorewa a Najeriya, an faddakar da mahalarta taron kan samar da kyakykyawan ginshiki na nuna adalci ga kowa da kauda cin hanci da rashawa da kuma hana musayan kudi lokacin zabe.

A lokacin da yake gabatar da kasida a wurin taron bitar, Farfesa Dakas Clement Dakas, ya ce addini tafarki ne na yin gaskiya.

Shugaban kungiyar House of Issachar, Barista Yakubu Sale Bawa, ya ce sun shirya taron don zaburar da al’umma aiwatar da hakkin kawo sauyi a sha’anin gudanar da harkokin shugabancin da Allah ya basu don walwalar ‘yan Najeriya.

Saurari cikakken rahoton wakiliyarmu Zainab Babaji daga Jos:

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:36 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG