Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Al’ummomin Irigwe Da Bace Sun Sa Hannu A Yarjejeniyar Zaman Lafiya


Al’ummomin Irigwe da Bace dake karamar hukumar Bassa a jahar Pilato sun yi wata yarjejeniyar zaman lafiya don ci gaban yankunan su.

Al’ummomin sun yarda suyi amfani da sulhu wajen magance matsalar kan iyaka, tsaida ayyukan bata gari dake haddasa kashe-kashen jama’a da lalata dukiyoyinsu, da kuma yaki da yawaitar makamai a yankin.

Shugaban raya al’ummar Irigwe, Sunday Abdu, wanda ya karanta yarjejeniyar a madadin al’ummomin biyu ya bukaci hukumar shata kan iyaka ta kasa da ta sake duba batun kan iyakar al’ummomin biyu.

Ga cikakken rahoton Wakiliyar Muryar Amurka a Jos, Zainab Babaji.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:33 0:00
  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG