A baya, fadar shugaban kasar ta tsara kasafin kudin na bana akan naira tiriliyan 20.51.
Rahoton ya kara da cewa, kilo daya na shinkafar gida ya karu da kashi 18.95, abin da ke nufin farashin ya karu daga naira 421 a watan Nuwamban bara zuwa naira 500.80 a watan Nuwambar 2022.
Taron na mayar da hankali ne kan yadda za a hada kai don bunkasa harkokin cinikayya da saka hannun jari da zai ciyar da tattalin arzikin Afirka gaba don a dama da nahiyar a fagen kasuwancin duniya.
A cewar Nnori, jiragen kasan yanzu za su tashi minti 30 kafin lokacin tashinsu da aka tsara a baya.
Bankin CBN ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su kwantar da hankulansu a game da tsarin saboda an yi ne don ci gaban kasa, ba wai don kuntatawa al’umma ba.
Yayin da wasu ke yaba wannan sabon tsari na cire kudade a bankunan kasar, wasu kuwa akasin hakan suke nunawa.
Hukumar kwastam ta ce a fili ta ke gudanar da gwanjan kaya kuma kowa zai iya shiga yanar gizo ya ga yanda a ke gudanar da cinikin.
Gidajen gyara hali a Najeriya, na ci gaba da kasancewa matattarar masu aikata laifuka mabambanta inda wasu masu laifi kan iya koyon wasu laifuka na daban musamman wadanda ba su da aikin yi kafin a kai su kurkuku.
Watanni shida da cikar wa'adin mulkin shugaba Mohammadu Buhari, bincike ya nuna cewa jimlar basussuka da gwamnatin Tarayya ta ciwo da sauran lamuni da ta yi sun kai Naira triliyan 71.5 amma masana tattalin arziki sun bayyana ra'ayi mabanbanta akan haka.
Rahotanni sun ce filayen Kalmoni da za a kaddamar da aikin, na dauke da arzikin man da yawansa ya haura sama da ganga biliyan daya.
Shugaban na Najeriya ya yi la’akkari da yadda wannan matsala ta samun kudaden ketare a farashi daban-daban take haifar da cikas ga tattalin arzikin kasa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.