Makwanni bakwai gabannin gudanar da zabe a Amurka, shugaba Donald Trump ya yi ikirarin cewa ya yi abin a zo a gani wajen yaki da annobar coronavirus da kuma dakile yawan mace-mace a kasar.
Shugaban Amurka Donald Trump ya ba da sanarwar cewa Daular Bahrain ta amince da Isra’ila a matsayin kasa, biyo bayan irin wannan yarjejeniya tsakanin Isra’ila da Hadaddiyar Daular Larabawa a watan da ya gabata.
Kamar yadda Amurkawa su ka saba kowace shekara, yau ma su na alhanin mutuwar mutane wajen 3000 a harin ta'addancin nan na ranar 11 ga watan Satumban 2001.
An dakatar da gwaje-gwajen maganin riga kafin COVID-19 na kamfanin AstraZeneca, abinda Dr. Fauci ya ce hakan ya nuna cewa ana kokarin tabbatar da ingancin magungunan.
A yau Laraba hukumomi sun yi gargadin cewa gobarar dajin da aka kasa shawo kanta na can na ci a jihar California, kuma ta yiwu iska ta kara tsananta gobarar.
Yayin da kasar China ke cigaba da tilasta tsiraru da wasu rukunin al'ummarta ayyukan da su ka wuce kima don amfanarta, gwamnatin Shugaban Amurka Donald Ttrump na shirin haramta sayen kayan da China ta sarrafa da gumin wasu al'ummominta.
Yayainda Amurka da Manyan kasashen duniya ke rige-rigen samar da alluran rigakafin cutar COVID-19 don kawar da annobar a doran kasa, al'amarin ya zama abin sukar juna tsakanin yan takarar shugabancin Amurka gabanin zaben na ranar 3 ga watan Nuwamba.
Lauyoyin mutumin nan da ya kirkiro kafar kwarmata bayanan sirri ta Wikileaks Julian Assange, da lauyoyin gwamnatin Amurka, sun buga muhawara a wata kotun birnin London a yau dinnan Litinin.
Jami’ar George Washington ta Amurka tana bincike akan wata Farfesa a sha’anin tarihi, da ake zargin ta amsa cewa ta yi shigar burtu a zaman bakar fata ba bisa ka’ida ba a duk tsawon rayuwar aikin ta.
Goyon baya da babban lauyan gwamnatin Amurka, Mai shari’a William Barr ke baiwa shugaba Donald Trump akan batun kiyaye doka da oda, da yake jadadawa a yakin neman zaben shugabancin kasa, ya haddasa muhawara akan rawar da ta dace ma’aikatarsa ta taka a harkarkokin siyasa.
Domin Kari