Wasu daga cikin ‘yan takarar da ke neman kujerun majalisar karkashin jam’iyyar Republican, sun fi karkata hankulansu ne kan yadda sahihancin zaben zai kasance, inda suke ta nanata ikirarin tsohon shugaban kasa Donald Trump, wanda ba tare da wata hujja ba, yake cewa an tafka magudi a zaben 2020.