'Yan Republican a majalisar wakilai sun zargi Biden da cin moriyar hada-hadar kasuwancin iyalinsa a kasashen waje.
A yau ranar Litinin 11 ga watan Satumba ne Amurka ta cika shekaru 22 da aka kai mata hare-haren ta'addanci wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 3,000.
Dutsen Kilauea da ke tsibirin Big Island na Hawaii ya sake barkewa da aman wuta ne a yammacin Lahadin da ta gabata, inda a halin yanzu aman wutar da ya ke yi a kewayen dutsen ne kawai, kamar yadda hukumar binciken yanayin kasa ta Amurka (USGS) ta sanar a ranar Lahadin da ta gabata.
Akalla mutum 16 ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata a ranar Laraba, bayan da Rasha ta yi luguden wuta kan wata kasuwa a wani birni a gabashin Ukraine, in ji jami'ai.
Uwargidan shugaban Amurka Jill Biden ta kamu da cutar COVID-19 kuma a halin yanzu tana fama da alamu masu sassauci, in ji Fadar White House a ranar Litinin.
Mataimakiyan sakatarin harkokin wajen Amurka mai kula da sha'anin Afrika Molly Phee ta bayyana cewa Ghana da Amurka za su ci gaba da hada hannu wajen tabbatar da mayar da dimokradiyya a Nijar.
'Yan takarar shugabancin Amurka na Jam'iyyar Republican sun fara muhawara a daren Laraba a babban taron farko na zaben Shugaban kasa na shekara mai zuwa.
Masu shigar da kara a Amurka sun sanar da cewa, an tasa keyar wadansu matasa ‘yan Najeriya biyu daga cikin uku da Hukumar FBI ke nema zuwa Amurka, wadanda ake tuhuma da laifin razana matasa samari da ‘yanmata a Michigan da kuma wadansu sassan Amurka don biyan toshiya ko su kunyata su.
Shi dai yankin na Hawaii, kan yi tunkaho da kasancewa yankin da ya fi ingantattun hanyoyin kare aukuwar hadurra a duniya.
Dubban mazauna Hawaii ne suka dinga tserewa daga gidajensu a Maui yayin da wata gobara ta mamaye tsibirin, inda ta lalata sassan wannan gari da ya shafe shekaru aru-aru tare da kashe akalla mutum 36 a wata gobarar daji mafi muni da Amurka ba taba gani ba a shekarun baya-bayan nan.
Amurka, yau Talata, ta goyi bayan yunkurin da kasashen yammacin Afirka ke yi na maido da tsarin mulki a Nijar bayan juyin mulkin da aka yi a ranar 26 ga watan Yuli, ta kuma ce matakin diflomasiyya ya fi amfani da karfin soja.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.