Hakan dai na nufin an koma gidan jiya yayin da majalisar ta kwashe makonni babu tsayayyen shugaban da zai jagorance ta.
A Tel Aviv, shugaban Amurka Joe Biden ya dora alhakin fashewar da auku a Asibitin Gaza a kan dayan bangaren.
Shugaban Amurka Joe Biden zai kai ziyara Isra'ila da Jordan ranar Laraba domin ganawa da shugabannin Isra'ila da na Larabawa, yayin da ake fargabar cewa yakin Isra'ila da Hamas zai iya kazance wa ya mamaye yankin.
Dubban jama'a ne a wata unguwar Falasdinawa da ke birnin Chicago a ranar Litinin suka gudanar da jana’iza da karrama wani yaro Musulmi dan shekara 6 da aka kashe a wani yanayi da ake zargi na nuna kyamar Musulunci ne.
Gwamnatin jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya ta soma wani yunkuri domin ganin jama’ar jihar sun amfana da ilmi, arziki, wayewa da fasahar ‘yan asalin jihar da ke zaune a Amurka da ma sauran kasashen duniya.
Yayin da Isra'ila ke shirin kai gagarumin farmaki ta kasa a gaza, akalla Falasdinawa miliyan daya da suka rasa matsugunansu na fuskantar rikicin jinkai.
Isra'ila ta kara zafafa hare-haren sama da take kai wa a zirin Gaza tare da killace shi daga samun abinci, man fetur, da sauran kayayyakin more rayuwa.
Shugaba Joe Biden, a ranar Asabar din nan, ya yi Allah wadai da harin ba-zata da Hamas ta jagoranci kaiwa, wanda ya kashe daruruwan Isra'ilawa, yana mai cewa abubuwan da suka faru "na fitar hankali ne" kuma "abin takaici ne," kuma "babu dalilinsu" – sannan ya jaddada goyon bayan Amurka ga Isra'ila.
'Yan majalisar dokokin Amurka sun kada kuri'ar tsige kakakin Majalisar Wakilai daga mukaminsa, wannan shi ne karon farko da aka taba ganin haka a tarihin Amurka.
A yayin da aka fara taron shekara-shekara na Majalisar Dinkin D!uniya wanda ke samun wakilcin shugabannin duniya, masu harkokin kasa da kasa sun bukaci sauyi daga kasashe masu karfi zuwa kananan kasashe irin na Afirka.
Babban taron Majalisar Dinkin Duniya ya hado kan shugabannin kasashen duniya a birnin New York a wannan mako, inda tarukan da za a gudanar a ranar bude taron, za su mai da hankali kan kara kaimi wajen cimma muradun samar da ci gaba a duniya.
Biden ya yi ƙira da a sanya Najeriyar cikin mambobin ƙungiyar kasashen ta G20.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.