Asibitoci a duk faɗin Amurka suna jinkirin aikin fida na tiyata don samar da isassun ma'aikata da gadaje saboda hauhawar cutar COVID-19 nau’in Omicron dake yaduwa.
Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce adadin masu kamuwa da cutar COVID-19 a duniya ya karu da kashi 11 cikin 100 a makon da ya gabata idan aka kwatanta da satin da ya wuce, inda nahiyoyin Amurka ne aka fi samun karin.
Hauhawar adadin masu kamuwa da cutar a Amurka ya sa wasu jami’o’i da dama sun ayyana shirinsu na yin karatu daga gida, cikinsu har da Jami’ar Havard.
Jami'an kiwon lafiya a Amurka sun ce an gano mutum na farko da ya harbu da sabon nau'in cutar coronavirus na Omicron a California.
Wanda ya kirkiro kamfanin Tuwita (Twitter), Jack Dorsey ya ce ya ajiye mukaminsa na shugaban kamfanin sada zumuncin Twitter.
Daya daga cikin bayanan da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Anthony Blinken yayi a ziyarar da ya kai Najeriya shi ne albishir da ya yi wa kasar na cire sunanta daga jerin kasashen da ke tauye 'yancin addini, batun da ya dauki hankalin al'umma.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya yaye kallabin sababbin kudurorin Amurka sa'adda yake jawabi ga jami'an diflomasiyya da na gwamnatoci a sakatariyar kungiyar raya kasashen Afirka ta yamma wato ECOWAS a Abuja, babban birnin Najeriya, inda ya ke ci gaba da ziyara
Amurka da Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar aiki tare a bangarori da dama, inda kasar ta Amurka ta yi alkawarin taimaka wa Najeriyar wajen shawo kan wasu daga cikin dinbin matsalolin da take fuskanta.
A cigaba da ziyarar Afurka da ya ke yi, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken, ya isa Najeriya, inda zai dada bayyana manufofin Amurka game da Afurka.
Sakataren Harkokin Wajen Amurka ya isa kasar Kenya, kasa ta farko da ya yada zango a ziyarar kasashen Afrika uku da zai kai wannan makon.
Janar Colin Powell, wanda shi ne bakar fata na farko da ya rike mukamin Sakataren harkokin wajen Amurka ya mutu ne a ranar Litinin bayan fama da cutar COVID-19. Shekarunsa 84.
Powell ya rike mukamin sakataren harkokin wajen Amurka a tsakanin shekarun 2001 zuwa 2005 a wa’adin farko na shugaba George W. Bush.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.