Shugaban Amurka Donald Trump ya koma fadar White House jiya Litinin da yamma bayan shafe sa'oi 72 a kwance a asibiti inda ya yi jinyar cutar COVID-19.
A yayin da zaben Amurka na ranar uku ga watan Nuwamba ke dada matsowa, masu kada kuri'a da dama na amfani da damarsu wajen jefa kuri’unsu da wuri da kansu ko ta hanyar akewa da sako, a jihohin da suka ba da damar yin haka.
Mako guda bayan da mace-mace sakamakon coronavirus suka zarta miliyan 1, an samu sama da mutane miliyan 35 da suka kamu da COVID-19 a kasashen duniya, a cewar Cibiyar samar da bayanan Coronavirus ta Johns Hopkins.
Wani sabon bidiyo da Shugaban Amurka Donald Trump ya sake daga asibitin Walter Reed inda ya je jinyar cutar COVID-19, ya nuna halin da shugaban ke ciki bayan da aka kai shi asibitin a ranar Juma'a.
Shugaban Amurka Donald Trump da ya kamu da cutar COVID-19 ya aika sakon Twitter, yana mai nuna godiyarsa da kauna ga jama’a.
An dauki shugaba Trump da jirgi mai saukar angule zuwa wani asibitin sojoji da ke kusa da fadar White House jiya Jumma’a da rana inda ake kyautata zaton zai yi jinya na ‘yan kwanaki.
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da asubahin yau Jumma'a cewa shi da Uwargidansa Malania sun kama cutar Coronavirus
An dai fara muhawarar ce cikin fara’a, wacce ta jirkice ta koma ta musayar kalamai kan batutuwan da aka tattauna akai.
Hana aiwatar da matakin karin ya hada da sanya dala 50 don cika takardun neman mafaka a kasar, wanda da ya zama karon farko da Amurka zata caji kudi kan wannan.
Shugaban kasar Amurka na jam’iyyar Republic Donald Trump da abokin takararsa na jam’iyyar Democrat tsohon shugaban kasa Joe Biden, sun tafka muhawara a daren jiya Talata.
Amurkawa sama da miliyan 100 ake kyautata zaton za su kalli muhawarar farko tsakanin Shugaba Donald Trump na jam'iyyar Republican da Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Joe Biden na Jam'iyyar Demokarat.
Bayan kusan shekaru hudu da dan takaran shugaban kasa a waccan lokaci Donald Trump ya fuskanci tambayoyi a kan biyan haraji yayin wata mahawara da aka yayata a telbijin kasa baki daya
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.