Gwamnatin Shugaba Donald Trump ta amince za ta ba jihar California tallafi domin taimakwa wadanda bala’in wutar daji ya shafa.
Shugaban Amurka Donald Trump na jam’iyyar Republican da abokin adawarsa na jam’iyyar Democrat Joe Bidden sun koma yakin neman zabe ranar Juma’a 16 ga watan Oktoba bayan da kowannensu ya yi taron amsa tambayoyin masu kada kuri’a a wurare daban-daban wanda aka nuna ta talabijin.
Uwargidan shugaban Amurka Melania Trump tace danta Barron Trump mai shekaru 14 da haifuwa ya kamu da coronavirus amma tuni gwaji ya tabbatar ya warke, bashi dauke da kwayar cutar kuma.
Matar nan da Shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar don zama alkali a Kotun Kolin Amurka, Amy Coney Barret ta fuskanci jerin tambayoyi daga Sanatoci mambobin Kwamitin Majalisar Dattawan Amurka kan Harkokin Shari'a a rana ta biyu.
Wani rahoton kungiyar yaki da rashawa a manyan matakai na kasashen duniya, ya nuna cewa wasu manyan kasashe ba su hana kamfanoninsu bayar da cin hanci a kasuwannin duniya, Amurka da Burtaniya ne su ka fi aiwatar da dokar.
Yayin da aka zaku a samu maganin mugunyar cutar nan ta COVID-19, sai gashi daya daga cikin kamfanonin harhada magunguna da ke kan gaba wajen kokarin samun magungunan ya dan dakatar da gwaje gwajen maganin da ya ke yi.kan mutane.
A jiya Litinin ne aka fara sauraren bahasin tabbatar da Any Coney Barret wacce za a nada alkaliyar kotun kolin Amurka a Washington, inda Barrett ta fadawa majalisar dattawa cewa bakamata kotuna su shata tsari ba, kamata ya yi su bar wa shugabannin Amurka da majalisar dokoki.
Kwamitin shari'a na Majalisar Dattawan Amurka ya fara zaman tantance Amy Coney Barrett wadda Shugaba Donald Trump ya zaba ta zama mai shari'a a kotun kolin Amurka.
Duk da yake shugaban Amurka Donald Trump na fuskantar koma baya a kuru’un jin ra’ayoyin jama'a, to amma ya na ci gaba da samun goyon baya a yankunan karkara. inda manoma suke kuma suka samu taimakon da gwamnati ta yiwa sashen noma.
Muhawara da aka tafka tsakanin mataimakan 'Yan takarar Shugaban kasar Amurka da ta kasance daya tilo da zasu yi kafin zaben shugaban kasa, ta tabo batutuwa da dama da suke sosawa Amurka rai.
A cigaba da shirye shiryen zaben Shugaban Kasar Amurka da ke gabatowa, da daren yau Kamala Harris Mataimakiyar dan takarar Shugaban Kasa karkashin jam'iyyar Demokarat, da Mataimakin Shugaban kasa, Mike Pence na jam'iyyar Republican, za su buga muhawara.
Shugaban Amurka Donald Trump ya koma fadar White House jiya Litinin da yamma bayan shafe sa'oi 72 a kwance a asibitin sojoji na Walter Reed inda ya yi jinyar cutar COVID-19.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.