Misalin karfe biyar na yamma ran Talata agogon Najeriya, wasu ‘yan bindiga sanye da kayan sarki, kuma sun kaiwa mutane farmaki, da kuma bude wuta akan gidajensu a garin Kwandiga dake jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya, kuma sun kashe a kalla mutane 39 da raunata wasu, kuma sun kona gidaje da yawa.