Sanarwar da daraktan yada labaran shiyar Sokoto na Darikar Katolika, Rabaran Pascal Salifu, ya fitar a jiya Lahadi, tace an saki Suleiman wanda ya kasance limamin Cocin St. Raymond dake garin Dumba, a karamar Hukumar Gusau, ta jihar Zamfara, kuma yanzu yana samun kulawar da ta dace.