Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya kwatanta matsalar garkuwa da mutane da ake yawan samu a kasar a matsayin wata alama da ke nuna gazawar shugabannin kasar.
A watan Afrilun bana gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwar jihohi 31 da za su iya fuskantar matsalar ambaliyar ruwa.
Kungiyar bunkasa tattalin arzikin Afrika ta yamma da ake kira ECOWAS ta kammala babban taronta karo na 67 a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya tare da sake zaben , Shugaban Najeriya Bola Tinubu a matsayin mai jagorantar kungiyar.
Wasu al’umma da dama dai sun kasa bayyana kwanan watan kalandar Musulinci da aka tambaye su.
Gwamnatin Najeriya ta ce babu wani sharadi da zai sa kasar ta kauce wa dokokin ta a yarjejeniyar SAMOA da ta sa hannu a ranan 28 ga watan Yuni na wannan shekara.
Yayin da ake dakon majalisar dokokin jihar Sakkwato ta yi matsaya akan kudurin dokar nan da ya jawo ce-ce-ku-ce a kan batun masarautar Mai alfarma Sarkin Musulmi, jama’a na ci gaba da nuna goyon baya ga masarautar.
Majalisar dokokin Tarayyar Najeriya ta ce ba za ta yarda gwamnatin kasar ta shiga wata yarjejeniyar kudi da za ta take dokar kasa ba, biyo bayan tada jijiyar wuya da korafe korafe da aka yi kan rattaba hannu da Najeriya ta yi a wata yarjejeniyar Samoa na kudi dalar Amurka bilyan 150.
Ruwan sama babu kakkautawa da ake samu a baya-bayan nan ya sabbaba ambaliya a wasu jihohi da birnin tarayya Abuja, al’amarin daya sanya Ministan bukatar gwamnatocin jihohin kasar su tsananta kokarin da suke yi na yashe magudanan ruwa.
An nada alkalan kotunan Kanon guda 2 ne domin su shugabancin kwamitocin bincike akan dawo da dukiya da kadarorin al’umma da aka wawure da kuma binciken tashe-tashen hankulan dake da nasaba da siyasa da batan mutane.
Mijin alkaliyar Musa Gimba ya tabbatar da sakin na ta sai dai yace ana cigaba da yin garkuwa da ‘ya’yanta 3.
Rundunar ‘yan Sandan jihar Delta ta yi kira ga wadanda ake cin zarafin su a gidajen aure, musamman mata su kai kara a ofishin ‘yan Sanda mafi kusa a maimakon yin korafi a dandalin sada zumunta.
Domin Kari