Binciken da rundunar ‘yan sandan kasa da kasa (INTERPOL) ta gudanar ya nuna cewa duk bayan sa’a guda, ana fitar da dubban daruruwan dalolin haramun daga Najeriya zuwa sauran sassan duniya.
A yayin aikin hajji na bana dai, hukumar NAHCON ta kayyade kudin da maniyatta za su biya a kan dala dubu 5 da 692.25 a madadin wanda aka tsara a farko-farko na dala dubu 6 da 401.31 inda aka sami ragin dala 700 da centi 6 a bisa ana canjin naira zuwa dala a kan naira 456 a waccan lokaci.
A wata hira ta wayar tarho da gidan talabijin ta Channels, Shugaban karamar hukumar Konduga, Abbas Ali Abari, ya tabbatar da afkuwar lamarin sai dai ya ce bashi da adadin wadanda al’amarin ya rutsa dasu.
Masu zanga zangar nuna takaici game da matsalar yunwa da tsadar rayuwa a Najeriya sun fara daukar matakin datse babban titin Abuja zuwa Kaduna da sanyin safiyar ranar Litinin 29 ga watan Yuli.
Tinubu ya sanya hannu a dokar a Fadar gwamnati da ke Abuja a ranar Litinin a lokacin taron majalisar zartawa da aka saba yi a kowane mako.
An samu dogayen layukan man fetur a wasu manyan biranen Najeriya a ranar Litinin bayan da kamfanin mai na NNPC ya fuskanci matsalar samar da mai ga ‘yan kasuwa da gidajen man fetur na cikin gida.
Amurka da Birtaniya da kuma Canada sun fitar da sanarwar gargadi ga ‘yan kasashensu mazauna a Najeriya, kan su zauna cikin shiri kan yiwuwar barkewar rikici yayin zanga-zangar da aka shirya za a yi a kasar.
Masu sharhi kan lamuran yau da kullum da kuma wasu shugabannin al’umma na bayyana ra’ayoyi mabambanta kan shirin zanga-zanga da matasan Najeriya ke yi don nuna damuwa kan tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Ahmad Rufa’i, ya tabbatar wa da Muryar Amurka cewa, ‘yan bindiga sun sace Sarkin Gobir tare da dan sa.
Masana tattalin arziki a Najeriya na ci gaba da yin fashin baki kan tasirin takaddamar da ke wakana tsakanin kamfanin tace man Dangote da hukumar kula da cinikayyar mai ta Najeriya. Matatar man ta Dangote ta ce a watan Agusta za ta fara fitar da fetur din da ta tace a kasuwannin kasar.
Rahotannin sun bayyana cewa mabiya Dauda Kahutu Rarara a shafin sada zumunta na Facebook da yawa sun tura sakonnin neman a cire shafin mawakin daga dandalin, saboda wata wakar yabo da ya yi wa gwamnatin Najeriya kwanan nan.
Domin Kari