Hashem Safieddine, dan uwan ne ga Nasrallah kuma babban jami’in kungiyar ne da ake sa ran zai maye gurbin Nasrallah
Cibiyar yaki da cututtuka ta Najeriya CDC, ta ce cutar kwalara da mace-mace sun karu da fiye da kashi 200 a bana idan aka kwatanta da na bara.
Gwamnatin jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya ta tabbatar da cewa barayin daji sun kashe Sarkin Kanya Alhaji Isa Daya, kwana biyu bayan sace shi tare da mutane tara.
“Kafin rasuwarsa, Alhaji Umar Shehu Idris dai yana rike da mukamin Mataimakin Magatakardan Majalisar Masarautar Zazzau.” Sanarwar da masarautar ta fitar ta ce.
An samu nasarar kashe dorinar ruwa da ta kashe mai gadin lambun Sarkin Yauri, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi tare da raunata wani a garin Yauri a jihar Kebbi.
Sanarwar da kakakin hukumar alhazan, Fatima Sanda Usara, ta fitar tace, a aikin hajjin badi, “maniyata daga jihohi ko ‘yan jirgin yawo ba zasu samu rangwame ba wajen samun kudaden musaya daga gwamnati.”
Sanarwar da mai rikon mukamin daraktan yada labaran babban bankin, Hakama Ali, ta fitar a yau Talata, ta sake tabbatarwa al’ummar da aniyar bankin ta tabbatar da sahihanci da amincin tsarin hada-hadar kudin Najeriya.
Ya sha alwashin cewa sabanin makamantan wannan lamari da ya faru a baya, ba za’a kyale hakan ta shude ba kuma gwamnatinsa za ta hada gwiwa da hukumomin tsaro wajen zakulo wadanda suka aikata aika-aikar tare da gurfanar dasu.
Da yake yanke hukunci, Mai Shari’a Nwite ya tabbatar da tsagin da Abure ke yiwa jagoranci da kuma babban taron jam’iyyar daya gudana a garin Nnewi a watan Maris din daya gabata wanda ya samar da shugabancin jam’iyyar na kasa.
Sanarwar da babban daraktan hukumar kula da koguna ta Najeriya (NIHSA), Umar Ibrahim Muhammad, ya fitar tace madatsar ruwa ta Jebba na sakin rarar ruwa kamar yadda hukumar dake kula da madatsar ruwan Kainji ta tsara, inda zuwa yanzu ta ba da tazarar sentimita 53.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin ta hannun Kakakinsa Bayo Onanuga, Shugaba Tinubu ya kama sunan Fubara inda ya yi kira a gare shi da "shugabannin siysar jihar " da su tabbatar da doka da oda, kalaman da ba su yi wa Fubara dadi ba.
Mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a sanarwar da ya fitar a yau Litinin bayan da batagarin dake adawa da sakamakon zaben kananan hukumomin da ya gudana a Asabar da ta gabata suka banka wa wasu daga cikin sakatariyoyin kananan hukumomin jihar wuta.
Domin Kari