A watan Yunin da ya gabata aka rufe sakatariyoyin sakamakon takaddamar da ta kunno kai tsakanin kantomomin rikon dake biyayya ga gwamna Siminalayi Fubara da tsaffin shugabannin kananan hukumomin, wadanda ke biyayya ga Nyesom Wike, ministan babban birnin tarayya, Abuja.