Ya kuma bayyana dalilin da yasa gwamnonin arewa suka shawarci Shugaba Tinubu ya dan tsahirta kafin ya tura kudirorin masu cike da cece-kuce.
A jawabin Amnesty ta bayyana cewar wadanda aka kashe din sun hada da matasa 20, da dattijo guda da kuma kananan yara 2.
A yayin taron kolin, jami’ai daga kasashen 2 zasu rattaba hannu a kan yarjejeniyoyin fahimtar juna da dama.
Wasu al’ummomin arewa maso gabashin Nijeriya na fama da mastalar ingancin rayuwa, musamman abin da ya shafi ilimi da kiwon lafiya, kamar yadda wasu daga cikin mazauna yankin Modire de ke karamar hukumar Yola ta kudu a jihar Adamawa suka koka.
A dai dai lokacin da al'ummar duniya ke bikin zagayowar ranar yaki da cutar kanjamau, masana lafiya a Najeriya na cewa har yanzu kare iyaye mata daga harbar jariransu da kwayar cutar kanjamau na ci gaba da zama kalubale.
Duk da barazar bakawa gonakin wasu manoma wuta da 'yan-bindiga su ka yi a wasu yankunan Birnin Gwari makonni biyu da su ka gabata, sulhun da gwamnatin jahar Kaduna ta assasa ya fara aiki.
MASU SHARHI NA NUNA FARGABAR AMINCEWA DA SABON KUDURIN SAUBUNTA HARAJI NA SHUGABA TINUBU
Akalla mutane 100 ne, akasarin su mata suka bace, bayan da jirgin ruwan dake dauke da su zuwa wata kasuwar hatsi, ya nutse a ruwa, a yankin kogin Naija dake Arewacin Najeriya, cewar mahukunta a ranar Juma’a.
NNPCL) ya yi karin haske a kan cewa tsohuwar matatar man Fatakwal mai karfin tace ganga 60, 000 a kowace rana da aka farfado da ita a kwanakin nan na aiki ne a kan kaso 90 cikin 100, ba kaso 70 cikin 100 ba kamar yadda kungiyar masu gidajen mai ta Najeriya (PETROAN) ta bayyana ba.
Wata sanarwa dauke da sa hannun daraktan hulda jama’a na bataliyar, Laftanar Kanar Danjuma Jonah Danjuma ta ce kamen nasa nada nasaba da samamen da ake gudanarwa a yankin Neja Delta na yaki da satar danyen mai.
A baya an yi ta wasan buya tsakanin Bello da hukumar EFCC da ta shigar da karar shi kan zargin wawure kudaden jihar ta Kogi - zargin da ya musanta.
Yahaya Bello wanda ya yiwa kotun jawabi da kansa, ya shaidawa mai shari’a Emeka Nwite cewa an sanar da shi game da batun gurfanarwar ne a kurarren lokaci a jiya Alhamis 28 ga watan Nuwamban da muke ciki don haka bai samu damar sanar da lauyoyinsa ba.
Domin Kari
No media source currently available