‘Yan cirani 21 ne suka mutu, wasu 23 kuma suka bace bayan da wani kwale-kwalen da ke dauke da mutane 77 ya kife a gabar tekun Djibouti, lamarin da shi ne na biyu cikin makonni biyu, kamar yadda hukumar kula da shige da fice ta Majalisar Dinkin Duniya ta sanar a ranar Talata.