Manyan jami'an diflomasiyya da kungiyoyin agaji sun yi taro ranar Litinin a birnin Paris, domin bullo da hanyoyi na taimakon jin kai ga kasar Sudan da ke arewa maso gabashin Afirka, wadda ke daf da fuskantar matsananciyar yunwa, domin gudun sake fadawa cikin mawuyacin hali.