Kotun tsarin mulkin kasar ta yanke hukuncin daurin watanni 15 a gidan yari da aka yi wa Zuma bisa samunsa da laifin raina kotu a shekarar 2021, lamarin da ya haramta masa tsayawa takara a zaben da za a gudanar a ranar 29 ga watan Mayu.
Tsadar rayuwa da matsalolin tsaro na daga cikin batutuwan da aka tattauna akansu a wannan zama wanda a yayinsa aka kwatanta cewa lokacin bullo da ajandar tafiyar da al’amuran mulkin rikon kwarya bai yi ba.
A watan Disamba ne aka sake zaben Tshisekedi a matsayin shugaban kasa a wani zabe mai cike da rudani, wanda ‘yan adawa ke neman a soke shi.
‘Yan tawayen sun ce sojojin sun kuma kai hari shaguna da kuma kan wasu motoci a yankin na Kidal.
Bangarorin biyu sun yanke shawarar Amurka za ta janye dakarunta cikin 'yan watannin masu zuwa ba tare da bata lokaci ba.
A ranar Alhamis gwamnatin Sudan ta Kudu da kungiyoyin 'yan tawaye suka rattaba hannu kan "yarjejeniya" samar da zaman lafiya a yayin tattaunawar neman sulhu a kasar Kenya, wanda aka bayyana a matsayin muhimmin mataki na kokarin kawo karshen rikicin Sudan ta Kudu da ya durkusar da tattalin arzikinta.
Ministan Ma’adinan jamhuriyar Benin a yayin wani ganawa da manema labarai yace kasarsa ta amince wa Nijar ta fara loda danyen man kan jirgin farko a matsayin matakin wucin gadi a bisa la’akari da yarjeniyoyin da ke tsakanin kasashen biyu.
Wata tawagar jami'an gwamnatin Amurka ta isa Jamhuriyar Nijar da daftarin da ke dauke da fasalin da Amurka ke fatan ganin an yi amfani da shi wajen kwashe dakarunta daga Nijar kamar yadda hukumomin mulkin sojan CNSP suka nuna bukata a watan Maris din da ya gabata.
Shugaban Ghanan, ya jefa wannan kalubalen ga takwarorinsa ne, a wajen bude taron koli na kwanaki uku kan kirkire-kirkire, tasiri da zuba jari, ko 3i Africa Summit a birnin Accra.
Gwamnatin rikon kwarya ta Jamhuriyar Nijar ta maida martani bayan da shugaban kasar Benin Patrice Talon ya dauki matakin hana lodin danyen man da Nijar ke shirin fara shigarwa kasuwannin duniya a tsakiyar watan Mayu.
Akalla mutum 90 aka samu tabbacin sun ji raunuka iri-iri a N’djamena, babban birnin kasar.
Alkaluman zaben sun nuna cewa Deby Itno ya samu kashi 61 cikin 100 na kuri’un da aka kada, yayin da Masra ya samu kashi 18.5 cikin 100.
Domin Kari