Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Amurka, Nijar Sun Tsawaita Tattaunawar Ficewar Dakarun Amurka


Sansanin sojin Amurka a Nijar
Sansanin sojin Amurka a Nijar

Bangarorin biyu sun yanke shawarar Amurka za ta janye dakarunta cikin 'yan watannin masu zuwa ba tare da bata lokaci ba.

Jami’an Amurka da na Jamhuriyar Nijar sun tsawaita tattaunawar da suke yi a hukumance kan ficewar sojojin Amurka daga kasar ta Nijar har zuwa ranar Juma’a.

Mataimakin Sakataren tsaro a fannin na musamman Christopher Maier da Laftanar Janar Dagvin Anderson, wanda shi ne Darekatan dakarun hadin gwiwa sun tattauna da wakilan sabuwar gwamnatin sojin Nijar a Niamey a ranakun Laraba da Alhamis.

Muryar Amurka ta ruwaito cewa tattaunawar ta kawo karshe a ranar Alhamis, amma jami’an Amurka da Na Nijar sun yanke shawarar tsawaita zaman har zuwa ranar Juma’ar da ta gabata a cewar wani jami’in tsaron Amurka wanda ya nemi a sakaya sunansa.

Bangarorin biyun sun yanke shawarar Amurka za ta janye dakarunta cikin watannin masu zuwa ba da bata lokaci ba.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG