A ci gaban rikicin diflomasiyar da ke tsakanin hukumomin Nijar da na jamhuriyar Benin, Shugaban Majalisar Sojoji ta CNSP ya ki ganawa da Ministan Ma’adinan Benin a wani taron masu ruwa da tsaki kan sha’anin man fetur da ya hada jami’an kasashen 2 a birnin Yamai.
An kama wani shugaban ‘yan fashi da makami a Najeriya da ake nema ruwa a jallo da yin garkuwa da jama’a tare da mutanensa 65 a kudancin Nijar, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar.
'Yan Afirka ta Kudu sun fara jefa kuri'a a zaben da ake yi wa kallon mafi muhimmanci a kasar a cikin shekaru 30, kuma wanda ka iya daga martabar dimokraɗiyyar ƙasar zuwa wani matsayi.
Jamus za ta ci gaba da barin tashar sufurin jiragen samanta na soji a Yamai a bude a mataki na wucin gadi, kamar yadda ma'aikatar tsaro a Berlin ta bayyana a yammacin jiya Talata, jim kadan bayan da Tarayyar Turai ta sanar da kawo karshen aikin soji a kasar nan da ranar 30 ga watan Yuni.
A jamhuriyar Nijar wani gidan talabijan mai zaman kansa wato Canal 3 Nijar ya kori ma’aikata sama da 30 bayan da suka tsunduma yajin aikin kwanaki 3 a makon da ya gabata.
Sama da fararen hula 20 ne aka kashe a wani hari da aka kai a tsakiyar kasar Mali a ranar Asabar, kamar yadda wani jami'in yankin ya fada a ranar Lahadi.
An kwashe sama da makwanni biyu ana gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da wata fitacciyar kungiyar sa-kai kan wani babban birnin da ke yammacin yankin Darfur inda aka kashe akalla mutum 123, in ji wata kungiyar agaji ta kasa da kasa a ranar Lahadi.
A ranar Alhamis ne aka rantsar da Janar Mahamat Idriss Deby Itno, wanda ya jagoranci mulkin sojan Chadi na tsawon shekaru uku, a matsayin shugaban kasa.
Kasar Benin ta toshe mashigar kan iyaka da Nijar ta ratsa tsakanin makwabta, kamar yadda majiyoyi suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa a ranar Alhamis, a wani tashin hankali da ya barke tun bayan da sojoji suka kwace mulki a Yamai a watan Yulin da ya gabata.
A ranar Alhamis 23 ga watan Mayu nan ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja zuwa birnin N’Djamena na Jamhuriyar Chadi domin halartar bikin rantsar da shugaban kasar Idriss Mahamat Deby Itno.
Lamarin ya faru ne da la’asar ta ranar Litinin 20 ga watan Mayun 2024 lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai harin ta’addanci kan sansanin soja a kauyen Boni na gundumar Makalondi da ke tsakanin iyakar Nijer da Burkina Faso.
"Kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada, a yau na gabatar da... murabus di na da na gwamnatin rikon kwarya, wanda bai da alaka da karshen zaben shugaban kasa na ranar 6 ga Mayu," in ji Masra a ranar Laraba a shafin X.
Domin Kari