Wasu ‘yan majalisar karamar hukumar Mangu a Jahar Filato sun tsige mataimakin shugaban karamar hukumar, Alhaji Garba Hassan suka kuma dakatar da shugaban karamar hukumar, Daput Minister Daniel na tsawon watanni uku.
Sakataren majami’ar ECWA, Rabaran Yunusa Nmadu ya shaida wa Muryar Amurka cewa ECWA, da ma sauran kungiyoyin addinin Kirista ba sa tilasta mutum shiga addinin, ba tare da amincewarsa ba.
A tsarin dimokradiyya, matsayin mataimakin shugaban kasa na da muhimmanci kamar na shugaban kasa, saboda shine ke rike shugabancin kasar, yayinda shugaban kasar ya shiga wani yanayi, ko dai na rashin lafiya, ko yayi murabus, ko ya rasu.
Bayan kammala zabubbukan fidda ‘yan takara da za su kara a zaben gama gari na shekarar 2023, hankalin jama’a yanzu ya karkata kan wadanda jam’iyyun zasu zaba a matsayin mataimakan shugaban kasa.
Kungiyar mambobin Katolika a Najeriya ta bukaci hukumomi su zakulo su kuma hukunta wadanda suka kashe masu ibada a majami’ar Saint Francis dake Owo a Jahar Ondo.
A cigaba da yunkurin da kungiyoyin al’umma ke yi don bada gudunmowarsu kan yaki da batagari da samar da tsaro, kungiyar kwararrun maharba a Najeriya ta horadda jami’anta fiya da dubu daya.
Jami’iyyar APC a Jahar Nasarawa ta zargi uwar jami’iyyar da neman haddasa rudani da rarrabuwar kawunan ‘ya’yan jami’iyyar a Jahar, biyo bayan sauya sunayen wassu deliget da zasu gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan takarkaru.
Rundunar sojin Najeriya ta jaddada kwarewarta wajen kakkabe burbushin ‘yan ta’adda da sauran kungiyoyi dake tada kayar baya da barazana ga tsaro a kasar.
Kungiyar hadin kan Kirista a Najeriya-CAN, reshen jahar Filato ta bukaci a rika yin hukunci kan duk wadanda suka aikata ba daidai ba, don samar da adalci ga kowa.
Shugaban kungiyar ta CAN a jihar Filato, Rabaran Fada Polycarp Lubo, ya ce za su gudanar da sujada da addu’o’i na musamman ne a ofishin kungiyar CAN.
Wasu mutane goma sha takwas dake neman takarar kujerar gwamnan jahar Filato a karkashin jami’iyyar APC, sun yi barazanar ficewa daga jami’iyyar tare da dimbin magoya bayansu, in har jami’iyyar bata dakile take-taken dora dan takara da basu amince da shi ba.
Gwamnan jahar Filato, Simon Lalong ya umurci jami’an tsaro da su kamo wadanda suka kai hari kan Sanata mai wakiltar Filato ta kudu, Nora Dadu’ut da wasu ‘yan jarida goma sha uku.
Rundunar ta ce ta kwato makaman ne a lokuta daban-daban yayin gudanar da aikinta na tabbatar da zaman lafiya.
Gwamnatin Jihar Nasarawa ta ce ta gano ma’adinan karkashin kasa fiye da talatin a Jihar, da take da yakinin sarrafasu zai janyo ingantan tattalin arziki da kawo saukin masifun rashin tsaro da Najeriya ke fuskanta.
Majalisar kolin Najeriya karkashin jagorancin shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta yi afuwa wa tsohon gwamnan jihar Filato, Sanata Joshua Dariye da tsohon gwamnan jihar Taraba, Jolly Nyame.
A yau Jumma’a ne al’ummar Kirista a fadin duniya ke fara gudanar da bukukwan Easter.
Bayanai daga wassu kauyukan karamar hukumar Kanam a jahar Filato na nuni da cewa mahara sun kashe mutane da dama a kauyukan dake yankin.
Rashin tsaro da ke ci gaba da lakume rayukan al’ummar Najeriya da haddasa asarar dukiyoyi da kara talauta ‘yan kasar, ya sa al’umma da daidaikun jama’a da ma kungiyoyin addinai ke ci gaba da janyo hankalin hukumomi kan su kara kaimi don kawo karshen rashin tsaron.
‘Ya’yan kungiyar Fulani mabiya Isa Almasihu sun jaddada batun hadin kan al’umma ba tare da nuna bambancin kabila ko addini ba, wanda a cewarsu zai zama mafita ga matsalolin tsaro da kasashen Afirka ke fuskanta.
Kungiyar Miyetti Allah a karamar hukumar Bassa da ke jahar Filato, ta bukaci hukumomi su yi bincike kan wani sabon salo na kisa da ake yi wa dabbobinsu, ta hanyar sanya musu guba a ruwa da abinci.
Domin Kari