Bayan doguwar cece-kuce yanzu haka an kawo karshen takaddamar sabon sarkin Jada, dake kudancin jihar Adamawa, inda yanzu aka samu sabon sarki Alhaji Umar Ardo.
Gwamnatin Somaliya ta ce an kashe Shugaban kungiyar al-Shabab na yankin Shabelle ta kasa da wasu mukarrabansa uku, a wani samamen da aka kai a kauyen Barire.
Koriya Ta Arewa ta ce ta sake damke wani ba-Amurke, wanda ta zarga da aikata laifi na yin karan tsaye.
Jiya Lahadi Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana da 'yan matan Chibok 82 dalibai, wadanda masu tsattsauran ra'ayin nan na Boko Haram su ka sace su, bayan da aka sako su ranar Asabar a arewa maso gabashin Najeriya mai fama da hankali.
‘Yan kungiyar BBOG sun kaure da murna a Dandalin Unity Fountain bayan labarin matan Chibok 82 da aka ceto sun shiga fadar shugaban Najeriya Aso Rock, inda suka gana da shugaba Buhari.
Biyo bayan nasarar da gwamnati Najeriya ta samu na cimma yarjejeniya da kungiyar Boko Haram, inda aka sako wasu daga cikin ‘yan matan Chibok har su 82 shugabannin da mutanen jihar Borno sun tofa albarkacin bakinsu.
Gwamnatin jihar Adamawa ta gudanar da bikin baiwa mai martaba sabon sarkin Shelleng Dr Abdullahi Isa Dasong sandar girma mai daraja ta daya, inda jama’a daga sassa daban-daban na ciki da wajen jihar suka halarta.
Gwmantin Somalia ta ce ta kaddamar da bincike a kan mutuwar Ministan Ayyuka da gyare-gyare, bayan da dogarawan tsaron wani jami’in gwamnati suka bindige shi har lahira.
Shugaban Amurka Donald Trump da shugaban Falasdinu Mahmoud Abbas sun dau alkawari a jiya Laraba a fadar White House game cimma matakan diflomasiyya wurin kawo zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.
Yan takarar zaben shugaban kasar Faransa Marine Le Pen da Emmanuel Macron sun gwabza a wata zazzafar mahawara ta sa’o’i biyu a talabijin a jiya Laraba, ana saura yan kwanaki kafin gudanar da zaben zagaye na biyu.
Jami’an harkokin kudi na Majalisar masarautar Kano sun bayyana a shedikwatar hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano, domin bada bahasi dangane da binciken zargin anyi ba dai-dai ba wajen sarrafa kudaden masautar cikin shekaru uku da suka gabata.
Yayin da a Najeriya hukumomi ke tallafawa wadanda rikicin Boko Haram ya shafa, hadakar kungiyoyin nakasassu a kasar na kukan cewa ba’a tunawa dasu.
Zuwa jiya Talata wasu tsauraran takunkumai, wadanda ka iya matsa lamba ga Koriya Ta Arewa ta fannin kudin shiga, sun kama hanyar zama doka, ta yadda ya rage mataki guda kawai.
Farar hula akalla 32 ne su ka mutu jiya Talata a wani harin ba-zata da ISIS ta kai daura da wani sansanin 'yan gudun hijira a Siriya a kusa da kan iyakar Iraki, a cewar wasu da abin ya shafa da kuma jami'an Kurdawan Siriya.
Batun ta’addancin Boko Haram a Najeriya shine ya mamaye taron da aka gudanar a jami’ar California, kan yaki da ta’addanci da ‘yan jaridu daga kasashen duniya suka halarta.
Kungiyar malamai ta kasa reshen jihar Adamawa ta ce dokar ta baci da gwamnatin jiha ta ayyana watanni shida da suka gabata bata yi tasiri ba.
Noma Tushen Arziki
Hukumar kare hakkin dan Adam a Najeriya da kungiyar direbobi ta NURTW sun yi kira ga shugabanin hukumomin tsaro a kasar da su gudanar da bincike game da matakin da gwamnatin jihar Taraba ke dauka a yanzu na iza keyar baki yanci rani da kuma karbe musu kudaden da ake zargin ana yi.
A jihar Bauchi hukumar ‘yan Sanda ta bayyana cewa an samu karuwar masu aikata fyade daga farkon shekarar nan, wanda yakai har an kama mutane 25.
Domin Kari