A ranar Juma’a ne likitoci a Kenya za su koma bakin aikin su, bayan sun amince da gwamnatin a kan yadda za a biya su sauran albashinsu da ya makale.
A ranar litinin ake kammala zaben shugaban kasar Chadi inda fararen hula suka fita rumfunan zabe, kwana daya bayan da sojoji suka kada kuri’unsu. Shugaban rikon kwarya Janar Mahamat Idriss Deby dai na fuskantar kalubale guda tara da suka hada da firaministan sa na yanzu.
Cikin wata sanarwar hadin gwiwa da gwamnatocin Burtaniya da Amurka suka fitar ta yi Allah wa dai da kashe-kashen fararen hula da aka yi a kasar Burkina Faso.
A ranar Litinin ne ake gudanar da zaben ‘yan majalisar dokokin kasar Togo bayan wani garambawul na kundin tsarin mulkin kasar, wanda ‘yan adawa ke cewa shi ne ya share fage ga shugaba Faure Gnassingbe na tsawaita mulkin iyalansa na tsawon shekaru da dama.
Tsohon dan Majalisar da ke wakiltar mazabar Enugu ta Arewa kuma tsohon shugaban kwamitin yada labarai na Majalisar Dattawa, Sanata Ayogu Eze, ya rasu. Sanata Ayogu, ya rasu yana da shekaru 66 a duniya.
A ranar Asabar Rasha ta ce ta kama mutane 11 - ciki har da ‘yan bindiga hudu, kan harin da aka kai a wani zauren raye-raye na Moscow da kungiyar IS ta dauki alhakin kaiwa, yayin da adadin wadanda suka mutu ya kai 115.
Biyo bayan umurnin shugaba Tinubu na gaggauta ceto daliban Kuriga sama da 280, babban hafsan tsaron Najeriya Janar Christopher Musa ya ce sojoji sun dukufa wajen ganin an ceto daliban da kuma hukunta ‘yan bindigan da ke wannan aika-aika, da wasu rahotanni
Mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar III ya sanar da ganin watan azumin Ramadan a Najeriya.
Domin Kari