Hukumar alhazan Najeriya NAHCON ta kara wa'adin lokacin biyan kudin ajiya don samun kujerar aikin Hajjin bana 2024 zuwa karshen watan nan na Janairu.
Kungiyar 'yan boko ta Tijanniyya wato "International Tijjaniyya Burotherhood" ta bukaci 'yan Izala su bar 'ya'yan kungiyar su sakata su wala wajen yin wazifa a masallatan jami'o'i.
"Ba ta yadda gwamnati za ta bari a yi irin wannan laifi ba ta hukunta wanda a ka samu da laifi ba." Ya ce.
Sabon shirin AREWA A YAU zai yi bitar wasu daga darussan da shirin ya tabo a shekarar nan ta 2023 mai bankwana. Daya daga shirye-shiryen shi ne dokar amincewa da kafa hukumar kula da almajirai da tsohuwar gwamnatin shugaba Buhari ta yi ta na jajiberin sauka daga mulki a karshen watan Mayu.
Hankali ya koma kotun kolin Najeriya a jajiberin sauraron daukaka karar gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, kan kalubalantar hukuncin kotun daukaka kara da ya soke zaben sa tare da bai wa abokin hamayyar sa Nasiru Yusuf Gawuna nasara.
Sabon shirin AREWA A YAU zai duba yanda zauren kwararru na arewa da ke bunkasa shiga fasahar ilimin na'urori da duniya ta tinkara 100% sun fara rangadin sassan arewa don wayar da kan matasa wannan hanya.
Fadar Aso Rock ta ba da tabbacin cewa shugaba Bola Tinubu zai tabbatar da an hukunta duk wanda a ka samu da sakaci har a ka samu yanayin mai ban takaici da tausayi.
Kungiyoyi da daidaikun mutane na nuna juyayi da bukatar bin kadun ma'abota halartar Maulidi a yankin Igabi a jihar Kaduna da bom din rundunar sojan Najeriya ya yi sanadiyyar mutuwar kimanin 30 a cikin su.
A yayin wata hira ta musamman da mai baiwa shugaba Tinubu shawara ta musamman kan al’amurran siyasa da aiyuka na musamman Ibrahim Kabir Masari, ya ki ya tabbatar ko ya karya ta labarin, ya ce, tone-tone a yanayin da a ke ciki ba zai taimakawa kasar ba.
Tuni 'yan Najeriya su ka caccaki wannan gagarumar tawaga ta shugaba Bola Tinubu da ta kumshi mutane 1,411 a taron na COP28, a yayin da gwamnati ke cewa ta na fama da karancin kudi.
“Saboda haka, jita-jitar da ake yadawa cewar zan amfana da sake dawo da yarjejeniya tsakanin Intels da Gwamnatin Tarayya ba gaskiya ba ne, wannan bata suna da kage ne kawai.”
NAHCON ta ce duk kamfani sai ya gabatar da shaidar mallakar Naira miliyan 30 a ajiye a banki da kuma ba da ajiyar Naira miliyan 25 don kare muradun alhazai idan an saba musu ka'ida.
A jawabin shi sabon jami'in yada labarai na kungiyar dattawan ta arewa da farfesa Ango Abdullahi ke jagoran ta, Malam Abdul'aziz Sulaiman, ya ce ya zama wajibi 'yan arewa su hada kai wajen kawar da bambance-bambance da fuskantar abubuwan da za su dawo da zaman tare a yankin.
Sabon shirin AREWA A YAU zai tabo alwashin mai taimaka wa shugaba Tinubu kan lamuran nakasassu Komred Muhammad Abba Isa, na janye masu bara daga kan tituna da ma dawo da masu nakasa na arewa da su ka shige jihohin kudancin Najeriya.
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya aikawa majalisar dokokin Najeriya takardar neman amincewarta domin ciwo bashin zunzurutun kudi dala biliyan 8.69 da kuma Fam miliyan 100.
Domin Kari