Magoya bayan ‘yan takarar shugabancin Najeriya na nuna yanda gwanayensu su ka yi zarra kan juna, yayin da kamfen din zaben 2023 ya fara kankama.
An samu mafi munin ambaliyar ruwa a ‘yan shekarun nan a Najeriya musamman in an kwatanta yawan mutanen da su ka yi asarar rayukansu. Mutuwar mutum 603 a fadin Najeriya ya ninka yawan wadanda su ka rasa rai a bara a sanadiyyar ambaliyar.
Ofishin dan takarar jam’iyyar NNPP Rabiu Musa Kwankwaso ya ce dan takarar na su ya ki zuwa zauren baje kolin manufofin ‘yan takara a gidan AREWA a Kaduna, don zargin taron na da manufar mara wa wani dan takara baya.
Mahmud Yakubu wanda ke magana a wata ziyara a Amurka a taron da asusun raya dimokradiyya da kuma asusun tallafawa tsarin zabe na duniya su ka shirya, ya ce labarun karya ya zama kalubale da ke kawo damuwa kan babban zaben Najeriya.
Ministan Cikin Gida na Najeriya Ra’uf Aregbesola ya ce Najeriya za ta rungumi hanyoyin kimiyya na tauraron dan-adam wajen kula da kan iyakokin kasar da tsawon su ya kai kilomita 5000.
Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana matukar takaici ga abin da ya zayyana a matsayin durkushewar al’adar karatun litttafai don samun ilimi mai inganci a tsakanin jama’ar da ke tasowa a wannan zamanin na yawaitar na’urorin sadarwa.
A wasu jihohin kamar Lagos an samu kimanin ‘yan takara 15 na gwamna daga jam’iyyu daban-daban ciki har da APC mai mulki da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
Shirin ya tattauna da Ahmed Ibrahim Lau da kuma shugaban kungiyar fataken masara ta yankin arewa Modibbo Sadik Nafada.
Kazalika matasa sun zanta kan mahangar su ga yadda za a aiwatar da lamuran tsaro ta yadda zai yi tasiri ba tare da cutar da sauran jama’a da ke zaune lafiya ba.
Rundunar sojan Najeriya ta bayyana cewa ta tona rijiyar burtsatse mai aiki da hasken rana a kauyen Rinze da ke Akwanga a Jihar Nasarawa ne don kyautata huldar sojoji da fararen hula da zai taimaka ga samun bayanan sirri da su ka shafi tsaron kasa.
Duk da bude damar fara yakin neman zabe da hukumar zaben Najeriya ta INEC ta yi, ‘yan takarar manyan jam’iyyu da ke alwashin shiryawa tsaf don tinkarar zaben 2023 ba su kaddamar da kamfe ba.
Shirin na wannan makon ya dora a inda ya tsaya a makon da ya gabata game da batun tsaro.
Ranar Larabar nan aka kaddamar da fara kamfen din ‘yan takarar shugaban kasa na babban zaben Najeriya da za a gudanar a watan Febrairun 2023.
Dage fara kamfen din jam'iyyar APC mai mulki daga Larabar nan zuwa wani lokaci nan gaba, ya haifar da yada raderadin cewa dan takarar jam’iyyar, Bola Tinubu, ne ba shi da lafiya.
Matsalar hare-hare da sace mutane don neman kudin fansa ta zama ruwan dare a sassan Najeriya inda ta hada har da Abuja, babban birnin kasar.
‘Yan Bokon arewacin Najeriya da su ka hada da malaman jami’a, ‘yan siyasa da jagororin addinai sun kaddamar da wata kungiyar da su ka yi wa taken “Arewa New Agenda” wato Sabuwar Alkiblar Arewa.
Shirin na wannan makon ya sake waiwayar kalubalen tsaro, musamman hanyar da za a magance matsalar satar mutane da ta zama ruwan dare da kuma sauran miyagun laifuka da ke yin barazana ga rayuka da dukiyoyin al’ummar jihohin arewa.
Alamu na nuna babbar jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta yi matsayar hakura da rarrashin gwamnan Ribas Nyesom Wike da ke cewa lalle sai shugaban jam’iyyar Iyorchia Ayu ya sauka daga mulki don kujerar ta koma kudancin kasar.
Shirin Arewa a yau na wannan makon ya ci gaba da tattanawa akan binciken ‘yan takara don ganin ayyukan da suka yi na taimaka wa al’umma.
Shugaban kwamitin amintattu na jam'iyyar PDP a Najeriya wanda ya yi murabus ya ce ya ajiye mukamin sa ne don samun sulhu a jam’iyyar, bisa korafin yawan mukamai a yankin arewacin kasar.
Domin Kari