A ranar Litinin jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara suka shigar da kara a kotun inda suka kalubalanci sabon wa’adin, wanda zai kare a ranar Juma’a mai zuwa.
Hukumomin tsaro a Najeriya, sun ba da tabbacin cewa za a gudanar da zaben 2023 lami lafiya suna masu kore duk wani yunkuri da wasu ke yi musamman a kafafen sada zumunta wajen yada kare-rayi don ganin sun haifar da fargaba a zukatan mutane.
Hankalin duniya ya karkata ga kai dauki Turkiyya da Siriya, inda mutane sama da 5,000 su ka rasu sanadiyyar girgizar kasa.
Duk da karin wa’adin da babban bankin Najeriya na CBN ya yi na kawo karshen amfani da tsoffin takardun naira, har yanzu jama’a a kasar na ci gaba da fuskantar matsalar karancin sabbin kudaden.
Karin kwana goman na zuwa ne yayin da ya rage kwana biyu wa'adin da aka diba na daina karbar tsofaffin kudaden ya cika.
Wannan al’amari ya faru ne mako guda bayan da wani jirgin kasan na Najeriya ya kauce hanya a jihar Kogi yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Warri daga Itakpe.
“Kowa ya kwan da shirin cewa, za mu yi duk abin da ya kamata don ganin an dawo mana da nasararmu.” Wani sako da Adeleke ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Juma'a ya ce.
Bankunan sun dauki wannan mataki ne don ba jama’a damar sauya tsoffin kudadensu yayin da wa’adin kammala amfani da su yake karatowa.
A halin da ake ciki, kotun ta ba INEC umurni da ta janye takardar lashe zabe da ta ba Adeleke ta ba Oyetola.
Angela Basset, ta kafa tarihi, inda ta zama ta farko daga kamfanin shirya fina-finai na Marvel da ta lashe lambar yabo ta Golden Globes da fim din “Black Panther: Wakanda Forever.”
To shin me ya sa ‘yan majalisar suka gaza zaben Kakakinsu, ko mene ne korafin ‘yan Republican da suka ki zabar dan jam’iyyarsu? Kadan kenan daga cikin abubuwan da muka tattauna tare da mai fashin baki Dr Nasir Danmowa.
Shirin Duniyar Amurka na wannan mako, ya yi bitar wasu daga cikin muhimman batutuwna da suka faru a wannan shekarar 2022 a Amurka.
Mai yiwuwa, nutsewar da wani kwale-kwalen ‘yan gudun hijirar Rohingya ya yi dauke da mutum 180, ya zamanto hadari mafi muni da ya auku a teku a ‘yan shekarun bayan nan.
Ana zargin Trump da tunzura magoya bayansa da suka kai hari a ginin Majalisar yayin da ake zaman tabbatar da nasarar da Joe Biden ya samu a zaben 2020. Sai dai Trump ya musanta zargin.
Wannan shi ne karo na uku da Argentina ke lashe kofin gasar, na farko a shekarar 1978 sai a 1986.
Najeriya na shirye-shiryen gudanar da babban zabe a watan Fabrairun badi, inda za a zabi shugaban kasa da ‘yan majalisar dokokin tarayya, sai kuma a watan Maris da za a yi zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha.
Hukumomin Amurkar sun ce za a gina tashoshin cajin ne a jihohi 35 da a sassan kasar a wani mataki na magance matsalar dumamar yanayi.
“Ka san makiyanmu suna bakin ciki ba mu samu matsala ba tsakaninmu da Mahamadou Issoufou, ji suke yi wai idan suka yi irin wadannan maganganu za su bata tsakaninmu.” In ji Bazoum.
Sakamakon wannan wasa na nufin Faransa za ta kara da Argentina wacce a ranar Talata ta doke Croatia da ci 3-0.
Wannan shi ne karon farko da wata kasa daga nahiyar Afirka da yankin kasashen larabawa, ta samu damar zuwa zagayen kusa da na karshe a gasar kofin duniya.
Domin Kari