Yayin da mazauna lardin arewacin Najeriya ke fama da kalubalen tsaro da tattalin arziki da kuma rashin ayyukan yi, an kafa wata sabuwar kungiya da nufin farfado da martabar yankin na Arewa.
Hukumar kula da hakkoki da karfafa gwiwar ‘yan kasa akan harkokin albarkatun mai da Iskar gas ta Najeriya ta ce damar da kamfanonin cikin gida masu hada-hada a bangaren albarkatun mai na kasar sun karu da kimanin kashi 30 cikin dari.
Yayin da ‘yan kungiyoyin gwagwarmayar shugabanci na gari a Najeriya ke caccakar matakan wasu gwamnonin arewacin Najeriya na rufe makarantunsu, dalibai a kwalejin nazarin ilimin aikin malinta ta Sa’adatu Rimi a Kano sun gudanar da zanga-zanga.
Hukumar da ke yaki da masa tu'ammali da ababen maye a Najeriya, ta ce ta samu daruruwan masu amfani da ababen maye a tsakanin 'yan takarar da ke neman mukamai a zaben kananan hukumomi da za a yi a karshen mako nan a jihar Kano.
Mazauna yankin arewacin Najeriya na bayyana halin kuncin rayuwa da fargaba da suke ciki saboda ci gaba da tabarbarewar yanayin tsaro a yankin. Sai dai masana da masu Nazari na sharhi akan dalilai da kuma hanyoyin bi domin magance matsalar.
Ziyarar wasu gwamnonin Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ga tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, na ci gaba da tada kura a fagen siyasar kasar.
Yayin da miyagu ke ta cin karensu ba babbaka a arewacin Najeriya mai fama da tsadar rayuwa, jama'ar yankin - kama daga masu fada a ji zuwa talakawa - na ta wayyo Allah.
Hukumomi a jihar Kano sun ce tashar samar da lantarki mai zaman kanta da gwamnatin jihar ke ginawa a madatsar ruwan Tiga za ta fara aiki a zangon farko na shekarar 2021.
Duk da cewa a jihar Kano ba a samu zanga zangar ENDSARS ko tarzomar fasa runbunan gwamnati ba, amma akwai tarin korafi kan zargin cin zalin da wasu ‘yan sanda suka yi wa fararen hula.
An kaddamar da aikin gwajin cutar hawan jini a wasu cibiyoyi a jihohin Kano Da Ogun a Najeriya.
A cigaba da dauke hankali da dambarwar zaben Amurka ke kara yi, tsohon gwamnan jahar Jigawsa kuma tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Sule Lamido ya ce lallai wannan al'amari na tattare da abin koyi ga kasashe masu tasowa kan muhimmancin hadin kai.
Majalisar dokokin jihar Kano ta bayyana damuwa akan yadda harkar ilimi a jihar ta kama tafarkin tabarbarewa saboda karancin malamai a makarantun jihar.
Kungiyar malaman Jami’o’I a Najeriya wato ASUU na dakon gwamnatin tarayya ta fitar da sakamakon gwajin tabbatar da sahihancin sabuwar manhajar da kungiyar ta samar wadda jami’o’in zasu rinka amfani da ita wajen sarrafa kudaden gudanar da ayyukan su.
Yayin da matasa ke kai farmaki kan rumbunan adana kayan abinci na gwamnati a wasu jihohin Najeriya, gwamnatin Kano ta kafa kwamitocin kula da lamuran tsaro a kananan hukumomi, a daidai lokacin da dattawan arewa ke ci gaba da jan hankalin matasan game da illar tarzoma.
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA zata gudanar da gwajin ta’ammali da miyagun kwayoyi da ababen sanya maye akan dukkanin ‘yan takarar shugabancin karamar hukuma da kansiloli a kananan hukumomin jihar Kano 44
Yayin da aka shiga mako na biyu matasa na zanga zanga a Najeriya domin nuna damuwar su dangane da yadda ‘yan sanda ke gudanar da ayyukan su da kuma lamura masu nasaba da rashin tsaro, kwararru na ci gaba da bayyana hanyoyin da ya kamata a magance matsalolin da masu zanga zangar ke magana akai.
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana gudurinta na fitar da kudi Naira Miliyan dubu biyu da dari uku domin gudanar da zaben Kananan Hukumonin 44.
Yayin da batun inganta wasu manyan hanyoyin a arewa maso yammacin Najeriya ke samun jinkiri, gwamnatin Kano na duba yiwuwar gudanar da aikin tare da sauran gwamnatoci, daga baya gwamnatin tarayya ta biya su.
Yau litinin daliban makarantun firamare da na sakandare a jihar Kano ke komawa ajujuwa domin fara daukar darasi bayan shafe fiye da watanni bakwai a gida sandiyya annobar Corona.
Bayanai na nuna cewa rashin cancantar daliban jahar Kano ta Najeriya ya haifar da tafiyar hawainiya ga kwalejin gamayya ta Jamhuriyar Nijar da jahar Kano ta Najeriya.
Domin Kari