Ministan harkokin cikin gida na kasar Turkiyya ya ce ‘yan sanda sun kama hodar ibilis mafi girma na uku a tarihin kasar.
Kasar Sin ta sanar da sanya takunkumai da ba kasafai aka saba gani ba a kan wasu kamfanonin tsaron Amurka biyu, saboda abin da ta ce na goyon bayan sayar wa Taiwan makamai.
Mutane 9 da suka hada da jariri daya ne suka mutu bayan kifewar kwale-kwalen da suke cikin a lokacin da suke kokarin tsallakawa tekun Bahar Rum a cikin yanayi mai hadari, kuma ana fargabar bacewar wasu mtuane 15, kamar yadda ma’aikatan tsaron gabar ruwan Italiya suka sanar a yau Alhamis.
A yau Alhamis, sojojin Isira’ila sun sanar da abin da suka kira, sababbi matakai da aka inganta na shigar da kayan agaji zuwa zirin Gaza, cikin har da gina wata sabuwar mashiga ta kasa a arewacin Gaza.
Likitoci a birnin Boston na jihar Massachusetts da ke Amurka sun ce sun yi nasarar aikin dashen kodar alade da aka canzawa kwayoyin halitta a jikin wani mutum majinyaci mai shekaru 62 da ke da ciwon koda a mataki mai muni.
Najeriya ta amince da dawo da hasken wutar lantarki ga jamhuriyar Nijar bayan janye wasu takunkumai da Kungiyar Raya Tattalin Arziki Kasashen Afrika ta Yamma, ECOWAS, ta yi kan kasar.
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirta ta Yamma, ECOWAS, ta amince da ta dage wasu takunkumai da ta kakabawa kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Guinea.
Domin Kari