Wata kungiya dauke da makamai ta kai hari a yayin wani bikin aure a tsakiyar kasar Mali tare da kashe akalla mutane 21, kamar yadda mazauna yankin suka fada a ranar Laraba.
Jam'iyyar Labour ta Birtaniya ta karbe mulki a yau Juma'a bayan shafe sama da shekaru goma tana adawa, yayin da 'yan adawa suka bai wa jam'iyyar gagarumar nasara.
A yau Alhamis ne 'yan Burtaniya suka kada kuri'ar zaben 'yan majalisar dokokin kasar.
Kungiyar Hezbollah ta kasar Labanon ta ce ta harba rokoki sama da 200 ne a wasu sansanonin soji da ke Isra'ila a matsayin ramuwar gayya kan harin da ya kashe daya daga cikin manyan kwamandojinta.
Matsanancin cunkoso da rashin mafita ne ya haifar da wani turmutsitsi a wani bikin addini a arewacin Indiya da ya hallaka mutane da dama, in ji hukumomi a ranar Laraba.
Guguwar Beryl ta ratsa kan ruwa a ranar Talata a matsayin wata mummunar guguwa mai rukuni 5 a kan hanyar da za ta bi kusa da Jamaica da tsibirin Cayman bayan da ta afkawa yankin kudu maso gabashin Caribbean, inda ta kashe akalla mutane biyu.
Wani hari da Isra'ila ta kai ya kashe akalla mutane tara a birnin Khan Younis da ke kudancin Gaza, a cewar jami'an kiwon lafiya na Falasdinu a ranar Talata.
Masu fafutuka a kasar Kenya sun yi kira ga masu zanga-zanga da su sake fitowa kan tituna a ranar Talata, inda da yawa suka yi watsi da rokon da shugaban kasar William Ruto ya yi na a tattauna bayan matakin da ya dauka na janye shirin kara haraji.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta tabbatar da sace wani direba da wasu mutane dauke da makamai suka yi a hanyar Ijebuode/Sagamu.
A cewar kwamishinan, mai yiwuwa maharan sun yi amfani ne da kan iyakokin jihar da babu tsaro wajen kai hare-haren.
Domin Kari