Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kalaman Shugaba Trump Game Da Harin Da Aka Kai Birnin London


Shafin Twitter na shugaba Trump
Shafin Twitter na shugaba Trump

A wata sabuwa kuma shugaban Amurka Donald Trump yace ya kamata duniya ta daina siyasa a yaki da ta’addanci, ya kuma yi nuni da mummunan harin da aka kai birnin London ya sabonta kiransa ga kotuna da su tabbatar da umarninsa na hana kasashe shida masu yawan Musulmi shigowa Amurka.

A furace furacen da ya sa a dandalin Twitter, shugaban na Amurka ya lashi takobin taimakawa Birtaniya ya kuma soki magajin birnin London kan ya dauki matsaya mai tsauri a kan yaki da ta’addanci.


Mr. Trump ya fada a jiya Lahadi cewar yakamata mu daina sa siyasa su mayar da hankali a kan aiki tsaron al’ummanmu. Ya ce idan bamu yi kaifin tunani ba, wannan abu zai kara ta’azzara.


Ya kuma yi wa magajin birnin na London Sadiq Khan shagube, wanda a bara ne aka zabe shi akan wannan mukami kuma shine Musulmin farko da aka taba zaba a matsayin magajin birnin wata babbar kasar yammacin duniya.


Kakakin Khan yace magajin garin na London bashi da lokacin mayar wa shugaba Trump martani.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG