Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

#EndSARS: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bayyana Goyon Bayan Buhari


Taron Gwamnonin Arewa
Taron Gwamnonin Arewa

Kungiyar gwamnonin Arewacin Najeriya ta ce ba za ta yadda da irin barnar da wasu ke da sunan zanga-zanga a Najeriya ba.

Gwamnonin Arewan da su ka kira wani taron gaggawa a jihar Kaduna sun ce ba su ji dadin abun da ke faruwa a wasu sassan Najeriya ba. Shugaban kungiyar gwamnonin Arewan kuma gwamnan Plato, Simon Bako Lalong shi ya yi magana a matsayin gwamnonin baki daya.

Yace abinda su ke bukata shi ne masu zanga zangar su jira su ga abinda gwamnati za ta yi a matakin jihohi da kuma gwamnatin tarayya. Ya ce gwamnati ba za ta lamunci yadda wadansu suke fakewa da zanga zangar lumana da matasa su ke yi na neman mafita su tada hankalin al’umma ba.

endsars-shugaba-buhari-ya-yi-jawabin-kwantar-da-hankali

endsars-matasan-arewa-sun-bukaci-gwamnati-ta-kawo-karshen-zanga-zanga

an-fafata-tsakanin-masu-zanga-zangar-endsars-da-yan-kasuwa-a-jos

Gwamnonin Arewan sun yaba da kauracewa zanga-zangar da wadansu matasan Arewa su ka yi sannan kuma su ka ce su na tare da shugaban kasa Muhammadu Buhari. Suka kuma bayyana cewa suna tuntubar gwamnonin kudancin kasar tare da jinjinawa gwaman jihar Lagos inda lamarin ya fi muni.

Jawabin shugaban kasa Muhammadu Buhari jiya Alhamis, da taron gwamnonin Arewa da kuma na gwamnonin kudu maso yamma dai sun sa wasu sa ran ganin wannnan zanga-zanga ta lafa a fadin kasar baki daya.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yana jawabi kan zanga zanga

Sai dai masu kula da lamura sun bayyana damuwa ganin shugaban kasar ya maida hankali kan matakan da ya ce gwamnatinsa ta dauka na yaki da talauci a kasar, a maimakon zanga zangar da ta rikide ta zama tashin hankali a wadansu sassan kasar, da kuma rasa rayukan masu zanga zanga da dama a jihar Ikko sakamakon amfani da karfin soji da jami’an tsaro suka yi kan masu zanga zanga a Lekki, lamarin da ya sa gwamnan jihar Babajide Sanwo-Olu ya kafa dokar hana fita ta tsawon sa’oi 24 kafin bada umarnin takaita zirga zirga na tsawon kwanaki uku da nufin shawo kan tashin hankalin.

Saurari Cikakken rahoton Isa Lawal Ikara cikin sauti:

#EndSARS: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bayyan Goyon Bayan Buhari-3:oo"
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:56 0:00


  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG