Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Nazari Kan Koma Bayan Ilimi A Kasar Ghana-Kashi Na Biyu-Nuwamba, 24, 2022


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Idan kuna biye da mu, shirin Domin Iyali ya gayyaci masu ruwa da tsaki domin nazarin matakan shawo kan koma bayan harkokin ilimi a arewacin kasar Ghana, daya daga cikin kasashen yammacin Afrika da binciken Babban Bankin Duniya ya nuna ana samun koma baya a fannin ilimin 'ya'ya mata.

Bakin da muka gayyata domin bada gudummuwa ga yunkurin neman mafita sun hada da Abdallah Tobodu: Kodinetan sashen ilmin addinin Musulunci na hukumar ilimi ta Ghana, da Gimbiya Ummul Khair Jafar: ‘yar jarida, da Samira Yahaya AbdurRahman: Babbar jami’a a hukumar wayar da kan al’umma ta kasa (NCCE). Issah Mairago Gibril Abbas: Mai fashin baki a kan al’amuran yau da kullum .

A shirin na yau, Gimbiya Ummul ta fara da bayyana faidar ilimantar da ‘ya’ya mata a ci gaban tattaunawar da wakilinmu a birnin Acrra Idris Abdullah Bako ya jagoranta.

Saurari cikakken shirin cikin sauti:

DOMIN IYALI: Nazari Kan Koma Bayan Ilimi A Kasar Ghana-Kashi Na Biyu
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:11 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG