Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

DOMIN IYALI: Koma Bayan Ilimin ‘Ya’ya Mata A Ghana-Nuwamba, 03, 2022


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Binciken da Bankin Duniya ya gudanar game da ilimin mata a shekarar 2018, na nuni da cewa, kashi 89 cikin 100 na 'yan mata a kasashen duniya suna kammala karatunsu na firamare, sai dai kashi 77 cikin 100 ne kawai suke kammala karatun sakandare. Binciken ya ci gaba da cewa, rashin ba ‘ya’ya mata damar samun ilimi mai zurfi yana janyowa kasashe asarar kudi tsakanin dala tiriliyan 15 zuwa dala tiriliyan 30 kowacce shekara.

Yau shirin Domin Iyali zai fara haska fitila a arewacin kasar Ghana, yankin da ake fuskantar koma bayan ilimin ‘ya’ya mata. Kafin mu kai ga hada kan masu ruwa da tsaki domin neman sanadi da kuma mafitan mun fara da yin shinfida da rahoto na musamman da wakilinmu Idris Abdullah Bako ya hada mana:

Saurari rahoton cikin sauti:

DOMIN IYALI: Koma Bayan Ilimin ‘Ya’ya Mata A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:10:14 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

XS
SM
MD
LG