Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Dan Sanda Ya Rasa Ransa Sanadiyar Rikicin Mallakar Gona a Jihar Gombe


wadansu gidaje da kungiyar Boko Haram ta lalata
wadansu gidaje da kungiyar Boko Haram ta lalata

Rahotanni daga jihar Gombe na nuni da cewa, wani jami’in dan sanda ya rasa ransa sanadiyar rikicin mallakar gona tsakanin al’ummomin kananan hukumomin Billiri da kuma Shongom.

Kakakin hukumar yan sanda a jihar Gombe DSP Obed Mary Malum ta shaida haka a hirarsu da Sashen Hausa, ta kuma bayyana cewa, kwamishinan yan sanda ya tura jami’ai a yankunan biyu domin kwantar da hankula.

Ta bayyana cewa an kona gidaje sha bakwai a garin Kufayi, banda haka kuma a kashe daya daga cikin jami’an ‘yan sandan da aka tura domin kwantar da tarzomar. Bisa ga cewarta, rikicin ya sami asali ne tun kaka da kakanni.

Ga cikakken rahoton da wakilinmu Abdulwahab Mohammed ya aiko mana

Rikici a jihar Gombe-1:24'
please wait

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Facebook Forum

XS
SM
MD
LG