Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Samu Karin Mutane Da Suka Kamu Da Cutar ZIKA A Jihar Florida


Zika Florida
Zika Florida

Jiya Litinin, cibiyar hana yaduwar cututtuka ta Amurka, ta gargadi mata masu juna biyu su guju kai ziyara wani yanki a jahar Florida, inda aka samu karin mutane da suka kamu da cutar Zika.

Jami'ai a jahar, sun gano karin wasu mutane 10 wadanda suka kamu da cutar, wanda ya yanzu ya kawo adadin wadanda suka kamu da cutar zuwa 10, lamarin da yasa Gwamnan jahar Rick Scott, ya nemi taimakon gwamnatin tarayya domin yaki da cutar.


"cibiyar hana yaduwar cututtuka ta tura jami'anta saboda su yi aiki tareda wakilan gwamna Scott a Florida. Inji kakakin fadar white House Eric Schultz, lokacinda yake magana da manema labarai jiya Litinin.


Gwamna Scott yace dukkan wadanda suka kamu da cutar sun harbu ne daga cizon sauro a cikin jahar.

XS
SM
MD
LG