Wani mutum ya harbe mutane 10 a wani wurin shagalin bikin murnar sabuwar shekara ta kasar China a wani birni da ke gabashin birnin Los Angeles, kuma har yanzu ana nemansa ruwa a jallo a cewar ‘yan sanda.
Lisa Marie Presley, mawakiya kuma diya daya tilo ga fitaccen mawakin nan Elvis Presley, ta rasu jiya Alhamis bayan da aka garzaya da ita wani asibiti a yankin Los Angeles, kamar yadda mahaifiyarta ta bayyana.
Bayan wata mahaukaciyar guguwar da ta yi kaca-kaca da wasu yankunan California a Amurka, ana ta yunkurin shara tare da gyara barnar da ta yi a ranar Laraba, yayin da aka samu saukin saukar ruwan sama a yankuna da dama.
Kwamitin bincike na musamman a jihar Geogia ta Amurka, da ke binciken ko shugaban kasar na wancan lokacin Donald Trump da abokansa sun aikata wani laifi yayin da suke kokarin juya zaben da ya fadi a shekarar 2020 ya kammala aikinsa.
Bayan kwashe zagaye 15 ana kada kuri'a cikin kwanaki biyar ga dan jam'iyyar Republican mai sausaucin ra’ayi, daga karshe an zabi Kevin McCarthy a matsayin kakakin majalisar wakilan Amurka a yau Asabar.
Wannan dai shi ne karon farko cikin shakaru 100 da wanda ake ganin zai zama kakakin majalisar wakilai ya gaza lashe zaben kujerar a zagayen farko.
Kamfanin Twitter ya dakatar da hada dandalin da manyan shafuka irinsu Facebook da Instagram, da abokan hamayyarsa Mastodan, Tribel, Nostr, Post, da Truth Social na tsohon shugaban kasa Donald Trump.
Amurka na shirin bai wa kasashen Afirka dala biliyan $55B nan da shekaru uku masu zuwa, kamar yadda jami’an Fadar White House suka bayyana.
Sanarwar da ma'aikatar shari'ar Aurka ta fitar ta ce, an kwace shafukan yanar gizon 55 ne bayan da wani wakilin FIFA ya gano wuraren da ake amfani da su wajen watsa wasan ba tare da izinin hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya ba.
Masu rajin kare dimokradiya a jamhuriyar Nijer sun yi na’am da taron da ake shirin farawa a yau Talata 13 ga watan disamba a nan birnin Washington DC a tsakanin kasar Amurka da kasashen nahiyar Afirka.
A Najeriya, kwararru a fanin siyasar kasa da kasa da masanan harkokin zamantakewan dan Adam na tafka mahawara akan babban taron Amurka da shugabannin Nahiyar Afirka a daidai lokacin da ake haraman taron a safiyar Talatan nan a birnin Washington D.C.
Shugaban kasar Ghana, Nana Akufo-Addo ya bi sahun sauran shugabannin Afirka 49 zuwa birnin Washington D.C. domin halartar taron Amurka da shugabannin Afirka, wanda za a fara yau Talata, 13 ga watan Disamba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.