Majiyoyi sun ce Biden na shirin tafiya Saudiyya, tare da tafiya Turai da ma Isra'ila a karshen watan Yuni.
Kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito cewa dan bindigar ya harbe kansa bayan da ya kashe mutanen.
An ware ranar ce don karfafa muhimmanci kula da tsaftar jiki a lokacin da mace ke al’ada da kuma wayar da kan jama’a.
Dan bindigar da ya kashe mutane 21 ya shafe sa'a guda a makarantar firamare ta Robb kafin 'yan sanda su harbe shi
Wadanda suka shaida lamarin sun ce iyayen yaran da dan bindigar ya rutsa da su a makarantar, sun yi ta yi wa ‘yan sandan ihu da su kutsa cikin makarantar a lokacin harbin wanda ya auku a ranar Talata, amma hakan ya ci tura.
Shugaban Amurka Joe Biden ya ce tilas ne a dauki matakin kawo karshen asarar rayuka da ya zama ruwan dare a kasar sakamakon hare haren kan mai uwa da wabi da 'yan bindiga ke yi.
Gwamnatin Amurka zata kashe zunzurutun kudi har dalar Amurka miliyan $537, wajen gina ofishin jakadancinta mafi girma a duniya.
Babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi kira a jiya Lahadi ga hukumomin soja a Burkina Faso, Guinea da Mali su mika mulki ga farar hula cikin gaggawa, ya kuma tunatar da duniya da ta cika alkawuran “yanayi na gaggawa".
Gwamnatin Biden ta baiwa Najeriya damar siyan manyan jirage masu saukar ungulu na kai hare-hare na kusan dalar Amurka biliyan 1 duk da damuwar da kasar ke da ita ta zargin take hakkin bil adama yayin da kuma take fama da barazanar kungiyoyin 'yan bindiga da masu tsattsauran ra'ayi a arewacin kasar.
Farautar mutumin da ya kai harin kan mai-uwa-da-wabi da safiyar yau Talata a gundumar Brooklyn ta birnin New York ta hadu da tsaiko yau da rana yayin da aka gano kyamarar daukar hoto a tashar jirgin kasa na layin 36th street da ya kamata ta dau hoton maharin ta lalace.
Tun bayan da aka kai harin da safiyar yau Talata ake ta jiran cikakken bayanin halin da ake ciki, ganin cewa da farko an ce akwai bama bamai. To amma daga bisani hankula sun dan kwanta bayan da aka ce babu wanda ya mutu zuwa yanzu. Amma daga cikin wadanda abin ya rutsa da su, biyar na fama.
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a ranar Juma’a a Abuja, ya ce Najeriya a shirye ta ke ta yi maraba da karin kudirori da saka hannun jari kan fasahar lataroni, yayin da ya yaba shirin kafa Cibiyar Raya Afurka ta Microsoft, da za ta ci dala miliyan 200.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.