Yayinda hukumomi a jihar Yobe, arewa maso gabas a Najeriya ke cewa suna cigaba da daukar matakai, domin gani komai ya dai-daita a makarantun kwana a jihar, Iyaye da harin ranar Talata da harin ya rutsa da ‘ya’yansu a makarantar gwamnati na Yadi Buni, har yanzu suna cikin tashin hankali, biyo bayan rashin ganin ‘ya’yansu.