Biyo bayan tabarbarewar tsaro a Najeriya, musamman ma a arewacin kasar inda rigingimun ta'addanci, da kabilanci, da Fulani makiyaya da manoma, fashi da makamai da batutuwa da dama, shugaban Najeriya ya gudanar da taro da shuwagabbannin al-umma domin samo hanyoyin warware wadannan matsalolin.