Babban mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ya nemi a kamo shugabannin Isra’ila da Hamas a ranar Litinin, wadanda suka hada da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, kan irin matakan da suka dauka a yakin da suka kwashe watanni bakwai ana yi.
Fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta bayyana a ranar Litinin cewa ta yi marhabin da sanarwar da mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ICC ya yi akan shugabannin Isra’ila da Hamas.
Nadin Mokhbar na wucin gadi na bukatar samun amincewar jagoran addinin kasar Ayatollah Ali Khamenei.
Hakan na faruwa ne yayin da Benny Gantz yake barazanar ajiye aikinsa na mamba a kwamitin yaki idan Isra'ila ba ta sauya yadda take tafiyar da yakin na Gaza ba.
Gidan talbijin na State TV bai fadi abin da ya haddasa hatsarin ba wanda ya auku a gabashin lardin Azerbaijin.
A halin da ake ciki, Isra'ila na kokarin yi wa birnin Rafah kawanya, suna masu cewa birnin shi ne mabuya ta karshe ga mayakan Hamas.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya sauka yau Alhamis a birnin Beijing domin gudanar da ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Sin, a wani mataki na nuna hadin kai tsakanin kasashen masu kama karya a yayin da Moscow ke ci gaba da kai sabbin hare hare a Ukraine.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a ranar Laraba ya yi watsi da sukarsa da ake yi cewa ba ya shirin fuskantar dahir a zirin Gaza bayan yaki, yana mai cewa ba zai taba yiwuwa a shirya wani yanayi a yankin Falasdinawa da ke fama da rikici ba har sai an fatattaki Hamas.
Taiwo ta rasu ne a watan Nuwamban shekarar 2023 sakamakon mumunan raunin da ta samu a kwakwalwar ta bayan afkuwar mumunan lamarin a gidan su da ke Newmarket.
A cikin kwanaki masu zuwa, ana sa ran sojojin Amurka da ke gabashin tekun Bahar Rum za su hada karshen daya gefen harabar wata dirkekiyar tashar jirgin ruwa - mai tsawon filayen wasan kwallon kafa na Amurka guda biyar a gabar teku a arewacin Gaza.
Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell ya fada a ranar Litinin cewa gwamnatin Biden ba ta ganin akwai yuwuwar Isra’ila ta samu “cikakkiyar nasara” wajen fatattakar Hamas a yankin Gaza na Falasdinu.
Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Alhamis cewa barazanar da Amurka ta yi na hana makamai ba za ta hana Isra’ila ci gaba da kai hare-hare Gaza ba, lamarin da ke nuni da cewa za ta iya yin gaban kanta wajen mamaye birnin Rafah mai cunkoson jama’a ba tare da goyon bayan babbar kawarta ba
Domin Kari