Najeriya za ta kara da Kwaddebuwa a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afirka a ranar Lahadi, 11 ga watan Fabrairun da mu ke ciki bayan kasashen biyu su ka yi nasara a wasan kusa da karshe na gasar da suka fafata yau, Laraba, 7 ga watan Fabrairu.