Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin sanarwar da kakakinta, SP Grace Iringe-Koko, ta fitar mai taken: “zaben shugabannin kananan hukumomin da aka shirya gudanarwa a ranar 5 ga watan Oktoban da muke ciki.”
Yayin da yake ayyana barkewar annobar a cibiyar lafiyar idanu ta Maiduguri, kwamishinan lafiya na jihar, Farfesa Baba Gana, yace daga cikin samfur din mutane 200 da aka aike domin gwaji, an tabbatar da 17 daga ciki kwalara ce.
An garzaya da Bala zuwa cibiyar kiwon lafiya ta gwamnatin tarayya dake Birnin Kebbi a jiya Laraba, sai dai an yi rashin sa’a ya mutu sakamakon raunukan harsashin da ya ji.
A lokacin hada wannan rahoto, gwanayen ninkaya na ci gaba da aikin lalubo mutum sama da 100.
Masana tattalin arziki irinsu Dakta Isa Abdullahi Kashere na jami’ar tarayya da ke Kashere a jihar Gombe, na ganin cire harajin abu ne me kyau, kuma hakan zai saukaka hauhawar farashi a kasar, idan har gwamnatin ta ajiye kwarya a gurbinta
A cewar sammacin, tsohon gwamnan zai halarci zaman kotun na rana r 24 ga watan Oktoba domin amsa tuhume-tuhumen sannan zai gurfana ne tare da wasu mutane 2 da ake karar tare.
Mai Shari’a Aboki ta tsayar da ranar 10 ga watan Oktoba domin yin hukunci a kan bukatar, ta kuma bada umarnin like dukkanin shari’o’in dake da nasaba da wannan.
Yawan masu zanga-zangar ya janyo cunkoson ababen hawa a kan tituna.
A wasikar daya aikewa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibrin, wanda ya kasance shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulkin kasar, Atiku ya bukaci majalisun tarayyar Najeriya su yi nazarin shawarar tasa a aikin gyaran kundin tsarin mulkin da suke yi.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bullo da sabbin dabarun jan hankalin masu zuba jari a bangaren mai da iskar gas din kasar.
A yau Alhamis, masu ninkaya suka tsamo karin gawawwaki 8 daga cikin kogin da wani kwale-kwalen da mahalarta taron Maulidi ya kife a garin Gbajibo, na karamar hukumar Mokwa ta jihar Neja.
Domin Kari