Shelkwatan tsaron Najeriya ta ce an kashe wani kasurgumin dan ta’addan nan Mai Hijabi a wani aiki da dakarunta suka gudanar a jihar Jigawa a wannan mako.
JOHESU ta tsunduma cikin yajin aiki tsakanin ranar 19 ga watan Mayu zuwa 6 ga watan Yunin bara (2023), makonni 2 da suka kusan durkusar da harkar jinya a asibitocin gwamnati.
Gidajen man kamfanin NNPCL sun mayar da nasu farashin zuwa Naira 998 a jihar Legas da kuma Naira 1,030, a Abuja a jiya Laraba.
A cewar NLC, abin takaici ne a ce gwamnati ta bar wani kamfani mai zaman kansa yana kayyade farashin mai a kasar.
An yi gargadin yiwuwar samun ambaliya a daren Laraba ga kusan dukkan gabar yammacin yankin Florida, wanda ya kai tsawon kilomita 500.
Wike, wanda ya bayyana hakan a cikin shirin siyasar tashar talabijin ta Channels mai taken “Politics Today”, ya musanta zargin sabawa dokokin jam’iyyar saboda kin taimakawa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasar da PDP ta tsayar a zaben.
Hukumar zaben jihar filato ta bayyana cewar mutane 75 ne ke takarar neman kujerun ciyamomi, a yayin da 788 ke fafatawa wajen neman kujerun kansiloli a mazabu 355.
Rahoton baya-baya nan a kan jarin daya shigo Najeriya da hukumar kididdigar kasar (NBS) ta fitar ya nuna cewa jarin ketaren ya ragu da kaso 65.33 cikin 100 idan aka kwatanta da dala miliyan 86.03 da aka samu a irin wannan lokaci a bara.
Kudaden zasu baiwa kungiyoyi masu zaman kansu na Najeriya dana kasa da kasa damar samar da agajin gaggawa ga fiye da mutane 180, 000 a jihohin Borno, Benuwe, Adamawa da Yobe.
Domin Kari