An gudanar da taron karfafawa al’ummar zanguna kwarin gwiwar kasuwanci ko Zongo Startup Summit 2023, tare da yin kira ga matasa da su kasance masu halayen da suka dace, domin samun nasarar kasuwancinsu.
‘Yan ta’adda na kungiyar Ambazonia Defense Forces (ADF) sun dau alhakin wannan hari da aka kai a ranar bikin Kirsimeti da farar safiya.
Al-Hassan Bello, mai sharhi kan harkokin kasa da kasa da tsaro, ya ce amincewa da kudurin wata nasara ce ga yaki da ta’addanci a nahiyar.
Kasar Faransa ta kammala janye sojojinta ranar Juma’a bayan da sabuwar gwamnatin mulkin sojan jamhuriyar Nijar ta bukaci su fice daga kasar.
A cewar 'yan kasuwar, ko da yake sun sami ƙarancin ciniki a bara, amma wannan shekarar ta fi muni.
"An tabbatar da cewa an kashe Maalim Ayman ne a wani farmakin hadin gwiwa da sojojin kasar Somaliya tare da taimakon sojojin Amurka suka yi a ranar 17 ga watan Disamba," in ji Daud Aweis a shafinsa na X da yammacin ranar Alhamis.
A yau Juma’a 22 ga watan Disamba ayarin karshe na dakarun Faransa a Nijar ke koma wa gida, sakamakon takun sakar da ke tsakanin kasashen 2, Faransar ta bada sanarwar rufe ofishin jakadancinta da ke birnin Yamai.
“Halin da ‘yan Nijar ke ciki a yanzu jarabawa ce ta Allah ke nan. A kara hakuri. Abu na biyu lokaci ne da zamu yiwa kasarmu addu’a da shuwagabanimu mu kuma fata Allah ya baiwa Nijar zaman lafiya” a cewar Fasto Benjamin Bernard
Shugaba Patrice Talon na jamhuriyar Benin ya bayyana aniyar sake da maido da hulda a tsakanin kasarsa da kasashe makwafta wadanda suka fada karkashin mulkin soja.
Babban hafsan hafsoshin rundunar tsaron Najeriya Janar Leo Irabor, da tsohon babban hafsan hafsoshin mayakan Najeriya Laftanar Janar Farouk Yahaya da Darakta Janar na hukumar leken asiri na soji, Manjo Janar Samuerl Adebayo na daga cikin manyan sojojin da aka karrama a yayin bikin.
Batun takaddama tsakanin shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS, da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tnubu ke jagoranta da shugabannin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar na ci gaba da daukar hankalin masana da masu fashin bakin kan sha’anin siyasa da diflomasiyya.
Domin Kari