Daruruwan ‘yan tawaye na kungiyar MJRN dake fafutukar ganin an dawo da tsohon shugaba Mohamed Bazoum da sojoji suka kifar a shekarar 2023 da suka fito daga kasar Libiya sun ajiye makamai tare da mika wuya ga mahukuntan kasar Nijar
Wani rahoto da wata kungiya mai zaman kanta ta kasa da kasa Equality Now ta fitar, ya ce ma’anar fyade a kasashen Afirka 25 ya ba da dama ga masu aikata laifuka su tafiyarsu ba tare da an tuhumesu wani laifi ba.
Sanarwar da wata kungiya mai rajin ceton bakin haure “Migrant Rescue Watch”, ta wallafa a shafinta na X, tace an kama mutanen ne a garuruwan Sabha da Bani Walid.
A yayinda wa'adin cika shekara da ficewarsu daga kungiyar CEDEAO, ministocin cikin gidan Nijar, Mali da Burkina Faso sun amince da sabon samfarin fasfo da takardun kasa da za a fara amfani da su domin yin bulaguro a maimakon fasfon ECOWAS da ake amfani da shi a yanzu haka
Tsama tsakanin kasar Faransa da Jamhuriyar na kara zafafa, yayinda sojojin da ke mulki a kasar suka kuduri aniyar sake wallafa tarihin kasar.
EU ta janye jakadan na ta ne domin ta ji ta bakinsa bayan da gwamnatin Nijar ta zarge shi da saba ka'ida da saka son rai wajen kasafta wani tallafin jin kai na Euro milion 1.3 da kungiyar ta bayar domin agaza wa 'yan Nijar da ambaliyar ruwa ta shafa.
A baya-bayan nan, an samu rikici tsakanin magoya bayan jam'iyyar NPP mai mulki da kuma babbar jam’iyyar adawa ta NDC, a unguwar Maamobi dake birnin Accra da kuma garin Ejura dake yankin Ashanti, wanda ya kawo damuwa ga shugabancin al’ummar Zango.
Shugabannin kungiyoyin kwadago da na jam’iyyun siyasa da jami’an fafutika masu yaki da akidar mulkin mallaka daga kasashen Afrika, Asia da na kudancin Amurka ne ke halartar wannan taro.
Tuni aka maye gurbinsa da tsohon ministan ci gaban karkara Kanal Abdoulaye Maiga.
A wani abinda ke fayyace alamun baraka a tsakanin hukumomin Mali, fira ministan gwamnatin rikon kwaryar kasar, Dr Choguel Maiga ya caccaki shugaban rikon kwaryar kasar, Janar Assimi Goita da mukarrabansa.
An yi garkuwa da wani fitaccen 'dan siyasar Uganda Kizza Besigye, bangaren adawa yayin bikin kaddamar da littafi a kasar Kenya a karshen makon daya gabata
Domin Kari