Shugabannin hukumomin kula da tattara bayanan sirri sun gudanar da taro a karkashin inuwar kwamitin kwararru na MDD, wanda tsohon shugaban Nijar Issouhou Mahamadou ke jagoranta don neman mafita ga matsalolin tsaro da ayyukan ci gaban al’umma a yankin Sahel.
A yayinda ma’aikatan kwadago suka tsunduma yajin aiki a kasar Faransa da nufin nuna rashin amincewa da matakin karin shekarun ritaya, a Jamhuriyar Nijar kuwa ma’aikatan kasar sun yi na’am da irin wannan mataki bayan da shugaba Mohamed Bazoum ya yi alkawalin kara shekarun ritaya daga 60 zuwa 62.
A Jamhuriyar Nijar kwamitin da aka dora wa alhakin nazarin hanyoyin magance matsalolin da ke dabaibaye ayyukan majalisar sansanta rigingimun syasa wato CNDP ya gabatar da rahotonsa a zaman da ya hada bangarorin siyasa da yammacin jiya Laraba.
A jamhuriyar Nijer matakin karin kudin datar internet ya haifar da damuwa a wajen jama’a musamman masu amfani da yanar gizo wajen gudanar da harakokinsu na yau da kullum.
Shugaban kasar Nijar ya ba da umarnin daukar duk matakan da suka dace don magance matsalar da ke faruwa a hukumar shige da fice da kuma ma’aikatar haraji ta kasar.
Hukumomin Jamhuriyar Nijar sun yanke shawarar rufe wasu kasuwanni a kauyuka da dama na Jihohin Tilabery da Tahoua, da nufin toshe hanyoyin da ‘yan ta’addar arewacin Mali ke amfani da su wajen samun kudaden shiga.
Wata sabuwar dambarwa ta taso a Jamhuriyar Nijar tsakanin ‘yan adawa da masu mulki bayan da shugaban Jam’iyar RDR Canji Alhaji Mahaman Ousman ya bai wa matarsa mukamin sakatariya a ofishinsa na tsohon shugaban kasa.
Ma’aikatar cikin gidan Jamhuriyar Nijer ta bayyana shirin fara rajistar kananan makaman da ke hannun farar hula da nufin karfafa matakan zuba ido kan makaman da ke yawo a tsakanin jama’a.
A jamhuriyar Nijer rahoton kungiyar addinin Islama ta kasa wato AIN ya yi nuni da cewa an samu raguwar mutuwar aure a birnin Yamai a shekarar 2022 idan aka kwatanta da adadin aurarakin da suka mutu a shekarar 2021.
Gwmnatin mulkin sojan Mali ta sanar da yin afuwa ga wasu sojojin Côte d’Ivoire 49 da ta kama a lokacin da suka sauka a filin jirgin saman Bamako a watan Yulin 2022.
Kasar Amurka ta bai wa jamhuriyar Nijar tallafin jirgin sama samfarin C 130 domin karfafa gwiwa ga sojojin kasar a yakin da suke kafsawa da ‘yan ta’addan yankin Sahel.
Tuni dai wannan al’amari ya haddasa mutuwar dubban kaji, abin da ya sa mahukunta suka dauki matakai don dakile yaduwar cutar.
Hukumomin Burkina Faso sun bukaci Faransa ta canza jakadanta Luc Hallade don maye gurbinsa da wani sabo.
Hukumomi a jamhuriyar Nijer sun cafke wasu manyan jami’an bankin Manoma na BAGRI, saboda zargin rubda ciki akan dubban miliyoyin CFA matakin da ya dauki hankalin kungiyoyin manoma da na jami’an yaki da cin hanci.
Masu sha’awar kwallon kafa a Jamhauriyar Nijar kamar sauran takwarorinsu na sassan duniya sun bayyana alhini a game da rasuwar fitaccen dan kwallon Brazil Pele.
A wani mataki na ganin jama'a sun dada samun kulawa daga gwamnati a Janhuriyar Nijar, an dau wani mataki na ganin cewa shugabannin hukumomin da su ka fi kusa da jama'a sun samu gogewa kan yadda za su yi aikinsu.
Hukumar kare hakkin dan adam a jamhuriyar Nijar ta yi bitar abubuwan da ta ce ta gano a yayin binciken da ta gudanar a mahakar zinaren Tamou dake jihar Tilabery inda wasu jiragen sojan kasar suka yi ruwan wuta a lokacin da suka bi sawun wasu ‘yan ta’adda a ranar 24 ga watan Oktoban da ya gabata.
A jamhuriyar Nijar ‘yan kasar sun bayyana juyayi a game da wani hatsarin da jirgi mai saukar angulu ya yi wanda ya yi sanadin mutuwar sojojin kasar biyu da wani sojan kasar waje lokacin da ya fadi ya kuma kama da wuta a filin jirgin sojan sama dake birnin Yamai a jiya litinin.
Domin Kari